Connect with us

KANUN LABARAI

Dalilai biyar da ke sa mata mantawa da Allah lokacin biki

Published

on

Zulaiha Danjuma

Galibin mata na shiga wani yanayi na mantawa da ibada lokacin shagulgulan biki, da har ta kan kai su mance da yin salla tsahon wuni guda.

Wani bincike da jaridar Kano Focus ta gudanar ta gano yadda galibin matan ke kin yin sallar saboda dalilan kwalliya, da yanayin hidimar bikin.

Sauran dalilan su ne yanayin kayan da matan ke sawa masu kama da tsirara, sai kuma hayaniyar wurin biki, da kuma uwa uba rashin son kada abu ya wuce su ba a yi da su ba.

Kwalliya (make-up) 

Wata matashiya Hauwa Ibrahim da jaridar Kano Focus ta zanta da ita, ta ce kwalliya ita ce abu na farko da galibin ‘yan matan ke sanyawa su kauracewa yin salla.

“Make-up yana cinkin abun da ke hana mata yin sallah a wurin biki saboda in akayi kwalliya ba a so a wanke ta” A cewar ta.

Nusaiba Magaji ita kuma cewa ta yi mata da yawa sun gwammace sallar ta wuce su da dai su wanke kwalliyar da ke fuskarsu.

“Make-up ne ke hana yawancin mata yin Sallah lokacin biki, wasu matan tun karfe 4 suke zuwa a yi masu kwalliya duk da cewa bikin ma sai 7 ko takwas za a fara.

“Ba zai yiwu ka bata irin wanna kudin da kuma lokacin ka ba, kuma a ce ka wanke lokaci kankani, kawai ya fi sauki mutum ya hade sallar ba ki daya kawai.” A cewar ta

Hidimar Biki

Ita kuwa wata budurwa mai suna Amira Sani ta ce wani lokaci kai

ne ke dukan zafi musamman ma idan al’amuran bikin suka yi yawa.

“Wasu mata zirga-zirgar da suke yi dan tabbatar da komai ya tafi yadda ya kamata ne ke sanya su mantawa da sallah

“Ko da ya ke hakan ba dalili bane, amma za ki ga wasu basa samun zama ne, saboda kujiba-kujiba” A cewar ta.

Matsewar kayan biki

Haka zalika wasu matan sun alakanta kaucewa yin ibadar da irin kayan da matan ke sawa da ko kadan ba za su basu damar yin sallar ba.

Amira Sani ta ce wani sa’in irin kayan da matan ke sanyawa basa kallon gabas ko kadan.

“Wasu matan hannun rigunansu ba dogo ba ne, ko kuma kayan ya matse, da ba zai yi sallah ba”.

“Wani lokacin kuma hannun kayan dogo ne amma ya matse ba zai bari a iya wanke hannu ba in za’ayi alwala.

“Ida za yi sallah dole sai dai a cire rigar baki daya, kuma samun wurin cirewar shima garari ne.” ta ce.

Hayaniyar wurin

Haka zalika dalili na gaba shi ne rashin samun wurin da babu kade-kade a lokacin bikin, shima na daya daga cikin abun da ke hana mata sallah.

Hauwa Sani wata budurwa ce a nan Kano da itama ta bayyana nata dalilan.

“Wata cewa za ta yi gurin sallah ne babu saboda cikin hall din ba wurin da za ta iya rakabewa tayi ba tare da hayaniya ba”

Haka zalika Farida Abubakar ta ce samun wuri mai nutsuwa abune mai wahala da biki, amma hakan bai zamewa mata hujjar kin yin sallah ba.

“In kin dauki Sallah da muhimmanci za ki samu yadda za ki yi duk hayaniyar wurin, duk da dai nasan yawanci wuraren biki babu wurin sallah” A cewar ta

Son ganin kwakwaf

Su kuma wasu matan sun ce rashin son kar a basu labarin yadda amarya ta shigo wurin biki ko yadda wani mawaki ya raira waka, kan sa su mancewa da ibada.

Hauwa Ibrahim ta ce wata in ta zo biki tanaso a ce anyi komai a kan idanuwanta, ko dan motsawa ba ta son yi dan ita a ganinta wani abu zai wuceta”

“Dan haka wata sai ta ajiye sallar dan gudun kar’ayi ba ita, sannan ta zabi hade sallolin idan ta koma gida.

Mahangar addini

Sai dai Kano Focus ta tuntubi babban malamin nan na Kano, Malam Abdallah Gadon Kaya, inda ya ce kwalliya ba laifi ba ne lokacin biki, sai dai kin yin sallah saboda kwalliya haramunne.

Ya ce mace za ta iya kwalliya idan ‘yan uwanta matane za su ganta, amma duk macen da saboda kwalliya ta kauracewa yin salla to ta saurari gamuwarta da Allah.

“Duk wacce tayi kwalliyar da ta san ba za ta yi sallah ba tana cikin fushin Allah”

“Babu babban fushi da ya fi mutun ya ki yin sallah, kuma wannan bikin Allah ba zai musa Albarka ba, kuma masu bikin ba lallaine Allah ya yi musu albarka ba, saboda an tozarta Allah, an tozarta shari’a Allah.

“Ibadar da ta fi kowacce muhimmanci an wulakantata a wannan bikin” A cewar sa.

Shawara

Malamin ya ba da shawarwari na kiyayewa da kuma samun yin sallah a yanayin biki.

“Idan makeup zai hana a yi sallah to a hakura da shi, ko ayi a wanke shi, idan lokacin sallah ya yi sai a koma ayi wani, a nuna cewa sallah ta fi make-up daraja, a wanke shi”

“In ba haka ba, ayi alwala sannan a yi kwalliyar a rike alwala, idan lokacin sallah ya yi ayi sallah ba sai an maimaita alwala ba” A cewarsa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending