KANUN LABARAI
Bikin Kirsimeti: Bai halarta musulmi ya taya kirista murna ba-Sheik Baban Gwale

Zulaiha Danjuma
Fitaccen malamin addinin Islamar nan da ke Kano sheik Abubakar Abdussalam Baban Gwale ya ce bai halarta musulmi na kwarai ya taya kirista murnar bikin kirsimeti ba.
Sheikh Abdussalam na yin wannan bayaninne ya yin zantawarsa da jaridar Kano Focus ranar Alhamis a wani bangare na bikin kirsimeti da ke gudana a yau Juma’a.
Shehin Malamin ya ce ko da yake duk wani abu da bashi da alaka da addini kai tsaye, kamar taya murnar aure, ko haihuwa, samun karin girma wanna ba laifi idan ka taya kirsta murna.
Amma ya ce dukkanin wani al’amiri da ya hada da addini da zai bayu izuwa girmama wancan addinin a kan musulunici to ba halak ba ne ga musulmi.

A cewarsa nuna farincikinka ga addinin kiristanci ya ci karo da koyarwar addinin islama, tunda dai addinin Islam aka ce ka yi riko da shi kai.
“Ba zaman fada ake ba, ana zaman mutunci ne, tayashi farin ciki indan ya samu wani abu na farin ciki kamar aure, promotion, ko haihuwa ba laifi bane.
Amma abun dayashafi krisimeti bai halalta a taya shi murna ba ko kadan.
“Idan shi ya taya ka murna a sallar ka, azuminka da laiyyarka, da hajjinka, toh shi wata kila a addinin sa ba a hana haka ba.
“Mu a addininmu cikin suratul Ma’idah, aya ta farko, Allah ya ce kada ku kuskura kuyi musayar amfani, ka amfana a amfanar maka, ka taimaka a taimaka maka akan abun da yake sabone ko kuma zalinci ne.
“Illa iyaka abun da musulmi zai iya yiwa abokinsa wanda ba musulmi ba shi ne, in sun dawo kace musu sannu da zuwa, sannu da dawo wa, kun dawo madallah shikenan.
“Amma abun taya murna na kirsimeti, da zaka fadi abinda suke fada na cewa suna murnan kirsimeti bai halatta ga musulmi ba” A cewarsa.
Ko cin abincin kirsimeti ya halarta
Shehin malamin ya ci gaba da cewa ba laifi ba ne cin abincin kirsimeti sai dai akwai sharruda kafin a kai baka.
Ya ce sharadin shi ne dukkanin naman da aka yanka dan meman kusanci lokacin kirsimeti to wannan bai halarta a ci ba.
Amma idan aka dafa abinci aka cudanya da mana wannan ba matsala ba ne, tunda dai ba naman da aka yanka dan neman kusanci a ka baiwa mutumba.
“Idan an kawo kyautar wani abu na ci ya halatta ka karba, kamar yadda mafi yawan malamai hamshakai, wadanda ke da zurfin ilimi suka bada bayani a cikin littatafan su.
“Abun shi ne naman da aka yanka dan neman kusanci wannan bai halatta mutun ya ci ba.
“Amma abinda ya halatta mutun ya ci shi ne abinci, misali abinci da nama, dama duk abunda aka hadashi da abinci wannan ba zai zama da matsala ba, tunda ba za a ce ka ci nama ba, abinci kaci kuma a ala’dance akan ci abinci hade da nama”
“Bisa al’adarmu a musulunce ai idan akayi yanka kuma akan farfasa naman ko a dafashi ko a soyashi sannan ayi kyautar sa.
“To suma zai iya zama haka a al’adar su, tunda akan samu hakan wani lokaci, wasu al’umma addininsu yana haduwa da al’ada sai kaga yadda abokanan zamansu musulmi ke yi suma haka suke yi.
“Ayi yanka a babbaka washegari a sassara sannan a soya a rabar irin wannan shi ne baza ka ci ba”
Ko musulmi zai iya yankawa kirsta dabba?
Malamin yaci gaba da cewa yin hakan ya danganta da dalili yankan da kuma niyar yin yankan.
Ya ce matukar yanka dabbar ka iya bayuwa izuwa ibada da neman kusanci ga Yesu al-masihu to ko kusa wannan yanka bai halartaba.
Ya ce amma yanka ba na ibadaba, kamar a ce kirista ya zo da kaza ko wani rago a yanka don a ci ba neman kusanci ba to wannan babu laifi.
“Idan dai ba yanka ne na ibadah ba, musulmi za iya tallafawa, kamar a ce anyi dan a ci abinci dashi, misali sunzo da kaji ko rago dan su dafa suyi abinci wannan ba laifi za ka iya taimakawa tunda suna yin haka”
“Amma idan yankane na ibadah kamar yadda mu layya yanka ne na ibadah, suma kuma suna da yankan ibadah, to idan yanka ne na ibadah ko na neman kusanci zuwa ga Yesu al-masihu to bai halatta ka shiga cikin wannan abun ba” A cewar sa.

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
