KANUN LABARAI
Mata a Kano na murna da kulle gidajen Kallo
Aminu Abdullahi
Mata da dama ne a nan Kano ke nuna farincikinsu tare da yabawa gwamnati kan matakin da ta dauka na kulle gidajen kallo a daukacin jihar nan.
Kano Focus ta ruwaito galibin matan na korafin yadda mazan ke shigar musu hakki matukar aka ce ana wasan kwallon kafa.
Wannan na zuwa ne a dai-dai lokacin da jama’a ke ci gaba da kiraye-kirayen a bude gidajen Kallon.
A cewarsu kulle gidajen kallon ba abin da zai haifar sai jefa al’umma cikin kunci da damuwa.

Gidan kallon ball na raba soyayya
Hussaina Adam wata budurwace a nan Kano ta ce gidan kallon ball ya sha sanyata fada da samarinta, a cewarta indai aka ce akwai ball to ko ba yadda za a yi samarinsu su je zance wurinsu.
“Duk lokacin da zaizo gurina matukar ya yi dai-dai da lokacin da za a haska wani wasa a gidan kallo baya zuwa.
“Sai ya ce min zaije kallon wasan Manchester, ko Real Madrid, a karshe ma sai dai mu sake tsai da wata ranar.
A gaskiya gidajen kallo na bata min rai,” a cewar ta.
Sakina Abdulmalik wadda matar Aurece ta ce, mijinta baya zama a gida da daddare matukar za a yi wani wasa to zai tafi gidan kallo.
Ta kara da cewa da zarar yadawo daga kasuwa da yamma, a nayin salar magriba yake fita zuwa gidan kallo, kuma ba zai dawo ba sai kusan karfe goma sha biyun dare.
“Kaga duk sanyin nan da akeyi sai yaje, amma jiya da daddare ba inda ya fita saboda an rufe gidajen kallon, wannan hukunci ne mai kyau,” a cewar ta.
Nafisa Tijjani itama wata budurwace a nan Kano, ta ce ta rabu da samari da dama sakamakon zuwa gidan kallon kwallon kafa.
A cewarta lazimtar kallon da suke yi ya sanya bata samun kulawar daga gare su.
Ta kuma ce idan da ace gwamnati za ta rufe gidajen kallon har a bada ma da tayi farin ciki da haka.
“Mu mata masu aure da marasa aure bama jin dadin gidajen kallon nan wallahi,” a cewar Nafisa.
Maza za su damemu da zaman gida
Su kuwa wasu matan cewa sukayi bai kamata gwamnati ta rufe gidajen Kallo ba domin wata hanya ce da ke samarwa maza nishadi.
Khadija Abba Garba ta ce kokadan bata ji dadin rufe gidajen kallon ba domin yana samar da nishadi.
Ta ce yanzu da aka rufe gidajen kallon mazajen su za su dinga damunsu da zaman a gida su kuma fara sa musu ido.
“Nikam bana goyan baya gaskiya, kaga wani lokacin ma mai gidana yana tafiya dani classic gurare da ake kallon kwallo.
Ko ina ra’ayin samari?
Sai dai a nan kuma magoya bayan kungiyoyin kwallon kafa a jihar Kano ne ke cigaba da kokawa kan yadda gwamnatin ta kulle gidajen kallon.
Hassan Ibrahim cewa ya yi baya goyan bayan rufe gidajen kallon duba da yadda harkokin wasanni ke daukewa matasa kewa tare da kara hadin kai a tsakanin su musamman idan suka je gidajen kallon kwallon kafa.
Ya kara da cewa idan har yazama dole a rufe gidajen kallon to yakamata gwamnatin ta raba musu da ta wacce za su rinka yin amfani da ita don kallon wasannin da akeyi ta shafukan internet.
“Ni kaga bamu da dammar da zamu iya kallon wasan kwallon kafa a gida don ba zamu iya siyan kati ba kuma ni masoyin kungiyar Manchester ne dole idan inaso na kalli wasan mu to sai nazo gidan kallo.
Aliyu Rabi’u Neymar ya ce bashi da gurin da a yanzu zai samu ya rinka kallon wasannin da ake haskawa na gida da na waje kasancewar an rufe guraren dake haska wasannin.
“Kaga dai bani da ilimin boka balle na kalla ta yanar gizo kamar yadda wasu ke cewa za su koma kalla ta internet to mu ya za ayi damu kenan.
“Idan nadawo daga gurin aiki idan dare yayi ba indai nake samun nishadi sama da gidan kallon, a cewar sa.
Muzammil Umar ya ce a yanzu zai koma kallon wasannin ne a gida tare da iyalansa saidai ya ce kallo a cikin mutane da yawa yafi dadi.
“Duk lokacin da na kalli wasa a gida bana samun nishadi kamar yadda zan fita waje. a kalla a cikin abokanai na muyiwa juna ruba,” a cewar sa.
Isma’il Kabuga ya ce rufe gidan kallo zai kawo koma baya ga harkokin wasannin ga matasa kasancewar gidajen kallon na debe musu kewa idan suka dawo daga kasuwa ko gurin aiki.
“Rufewar ba alheri bane don yanzu wasu za su koma zaman majalissa ai ta musu wanda daga karshe ma ai ta samun rigima a tsakanin.

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
