Connect with us

KANUN LABARAI

Yansanda a Kano sun kama wanda ya sassari matarsa a kotu

Published

on

Aminu Abdullahi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama mutumin da ya sassari matar sa mai dauke da juna biyu tare da wanta a harabar kotu bayan da mai shari’a ya raba auren su a ranar Litinin data gabata.

Kano focus ta ruwaito cewa mai magana da yawun rundunar Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan ranar Juma’a a anan Kano.

Kiyawa ya ce an kama Bilyaminu Abdullahi  mai shekara 48 bisa zargin yunkurin kisan kai ta hanyar sarar matar sa Shafa’atu Sale  wanta Ado Sale a harabar kotun shari’ar musulunci dake karamar hukumar Rano.

Da yake jawabi wanda ake zargi Bilyaminu Abdullahi ya ce ya aikata laifin da ake zargin sa akai ne sakamakon hukuncin da alkali ya yanke bai yi masa dadi ba.

“Alkali yace ya raba aure na da ita akan fansar naira dubu ashirin, duk da na fada masa cewa ni matata nake so ba wai kudinne yayimin kadan ba amma ya ce a tura a kwashe kayan ta.

“Abinda ya bata min rai kenan ana fitowa daga kotu na kama yankar su da wuka.

“Wuka tace ina sana’ar saida zuma ne kuma na yanke ta akanta da hannunta shi kuma na yanke shi a kafadarsa da hannun sa,” a cewar Bilyaminu.

Kotu a Kano ta yankewa gawa daurin shekara guda a gidan yari

Miji ya sassari matarsa a gaban kotu a Kano

An kafa kotunan sauraron korafin zaben kananan hukumomi a Kano

Ya kara da cewa wantane ya maida ita gida, da ya bibiya don jin ba’asi sai iyayen  da ‘yan uwanta suka nemi da ya sakar musu ‘yar su.

Ya kuma ce bayan da yaki amincewa ya sake ta ne, suka maka shi kara a gaban kotu da har takai ga alkali ya raba auren su.

A nata bangaren Shafa’atu Sale ta ce duka da cin zarafi ne yasa ta nemi da a raba auren nasu.

Ta kara da cewa bayan da suka fito daga kotune sai ya dinga kiran sunanta, kin amsawar da tayi sai ya zaro wuka ya fara caka mata akan ta da wuya da kuma hannu sannan ya koma kan wanta inda shima ya sassara shi.

Shafa’atu ta kuma ce ita ta nemi da a raba auren nasu inda kuma ta bukaci da abi mata hakkinta bisa raunukan da ya yi mata ita da dan uwan nata.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending