Connect with us

KANUN LABARAI

Idan muka fara ramuwa a kan ‘yan kudu abin ba zai yi dadi ba-Bashir Tofa

Published

on

Aminu Abdullahi

Shugaban kungiyar dattawan Arewa Alhaji Bashir Othman Tofa yayi Alawadai da kinsan da ake yiwa ‘yan arewacin kasar nan musamman Fulani a kuduncin kasar nan inda ya ce matukar aka fara ramuwa to za a sha wahala kafin a shawo kan al’amarin.

Kano Focus ta ruwaito cewa Tofa ya bayyana hakane cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai ranar Talata a nan Kano.

Ya ce ba abune da za a yarda dashi ba yadda ake kashewa tare da raunata al’ummar Arewacin kasar nan a yankin kudancin kasar.

Ya ce a bayyana yake cewa akwai mumunan shiri da wasu keyi da zai haifar da rikici da ka iya sanadiyyar ruguza kasar baki daya.

“Abubuwa sun fara daukar dimi matukar ‘yan Arewa suka fara daukar fansa akan al’ummar kudu dake zaune a nan tofa zai yi wuya a shawo kan al’amarin.

“Makiya na gida da na waje, wasu ma jami’an tsaro sun san su, suna kulla kullar yadda zamu ci zarafin junanmu, ta yadda ba zamu sake dawowa kamar yadda muke ba da zarar an fara zubda jini.

“Babu wani bangare a kasar nan da yake zaune lafiya.

“ ‘Yan ta’adda na cikin gida da makota dama na kasashen ketare nata kokarin yin duk mai yiwuwa don ganin sun ruguza mana kasa,” a cewar sa.

Haka zalika yayi kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya dauki matsalar tsaro da ta addabi kasar nan da kuma yadda ake kashe mutane ba gaira ba dalili da muhimmanci tare da daukar mataki na gaggawa don magance su.

“Nasan fadar shugaban kasa ta damu kuma ana tattaunawa akan batun amma akwai bukatar daukar matakai na gaggawa.

Ya kara da cewa idan har wani dan kasar nan ba shi da ikon yin rayuwa da gudanar da kasuwancinsa har sai an muzguna masa ko yi masa barazanar kisa a wani bangare na kasar nan, to babu wani mahaluki da yakamata a bari shima ya zauna a ko ina.

“Idan kuwa har hakane to bamu da kasa kuma wannan shi ne abinda makiyanmu ke fata kuma bai kamata mu bar suba.

“Wadancan shugabanni wawayene suda ‘yan amshin shatansu wadanda ke karfafa musu gwiwa korar wasu ‘yan kasa daga jihohin su,

“Ya kamata su tuna cewa suna da ‘yan uwa dake zaune a wasu sassan arewacin kasar nan.

“Dole ne su daina, ko kuma doka ta dakatar da su ta hanyar da ya dace,” a cewar sa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending