KANUN LABARAI
Ma’aikatan gwamnati a Kano suyi rijista da APC ko kuma….- Abdullahi Abbasa

Mukhtar Yahya Usman
Shugaban riko na jam’iyyar APC a jihar Kano Abdullahi Abbas ya gargadi ma’aikatan gwamnati da sauran masu amfana da gwamnatin Kano da su shiga jam’iyyar APC ko kuma a janyemsu dukan damar da suke samu.
Kano Focus ta ruwaito Abdullahi Abbas na wanna barazana ne ya yin kaddamar da fara rjistar zama dan jam’iyyar APC a jihar Kano da aka gudanar ranar Litinin.
Ya ce gwamnati ba za ta lamunci duk wani da ke aiki a karkashinta ba kma bashida katin zama dan jam’iyyar APC.
A don hakan ne ma ya bukaci dukkanin ma’aikatan gwamnati da masu rike da ofisoshin siyasa a fadin jihar nan, su tabbatar suna mallaki katin zama dan jam’iyyar APC.

Ya kuma ce ba wai su kadai umarnin ya hauba. ya zama dole su fito da iyalansu da ma duk wadanda suke da iko da su baki daya domin yin rijstar.
Jam’iyyar APC a Kano na yunkurin hallakani-Saha’aban Sharada
Zargin badakalar Tracker: Kotu ta ce a biya Bappa Babba N50,000 ladan bata masa lokaci
Idan ba tsoroba Abdullahi Abbas ya je ayi masa gwaji kwaya-Muazu Magaji
“Muna bukatar mutashi tsaye, mu tabbatar mun samu masarar yin rijistar mambobi da yawa a jam’iyyarmu ta APC
“Dukkan masu rike da ofisoshin siyasa, dukkanin ma’aikatan gwamnati, da dukan wanda ke kowanne irin aiki ne a karkashin gwamnatin Kano, ya zama dole su fito su yi rijista da jam’iyyar APC.
“Bama su kadaiba, harma da duk danginsu da abokansu da sauran wadanda suka isa da su, su sanyasu su yi rijista da jam’iyyar APC
“Ina kira ga gwamnan Kano da kada ya sake baiwa kowa aikin gwamnati har sai yana da katin jam’iyyar APC” a cewar Abdullahi Abbas

Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

Hausa
Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Nasiru Yusuf Ibrahim
Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.
Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.
Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.
A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.
Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Hausa
Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Nasiru Yusuf Ibrahim
Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.
Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.
Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.
A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.
