Connect with us

Hausa

Shekara guda a mulkin Kano, wacce rawa Aminu Ado ya taka

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

A ranar 9 ga watan Maris din shekarar 2020 ne gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya nada Alhaji Aminu Ado Bayero Sarkin Kano na goma sha biyar a dular Fulani.

Kano Focus ta ruwaito nadin Alhaji Aminu Ado Bayero ya biyo bayan tunbuke sarkin Kano na 14 a daular Fulani Malam Muhammadu Sunusi II da gwamnan ya yi.

Gwamnan dai ya tunbuke rawanin sarki Sunusi ne bayan da ya ce baya bin ka’idojin da saurauta da gadar, tare da rashin girmama na gaba da ma wasu dalilan.

Haka kuma bayan tunbukeshi ne gwamnan ya ayyana Aminu Ado a matsayin sabon sarkin Kano kuma shugaban majalisar sarakunan Kano baki daya.

Wanen ne Aminu Ado Bayero

An haifi sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero a rananar 1 ga watan Yulin 1961.

Mahaifinsa shi ne marigayi Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero, sarki na 13 a daular Fulani, da ya kuma kwashe shekara 51 yana sarautar Kano tun daga shekarar 1963 zuwa 2014.

Aminu Ado Bayero shi ne da na 2 a wurin mahaifinsa, ya yin da Sunusi Lamido Ado Bayero ke zaman babban wansu, sai kuma sarkin Bichi Alhaji Nasiru Ado Bayero ya ke biye masa a matsayin da na uku a wajen mahaifinsu.

Alhaji Aminu Ado Bayero ya fara karatun Islamiyya a gidan Dabo, inda a nanne ya koyi karatun alkur’ani, fiqhu da sauran litattafan addini.

Haka kuma ya halarci makarantar firamare ta Kofar kudu da ke gidan sarki, da ga nan kuma ya wuce sakandiren gwamnati da ke Birnin Kudu a jihar Jigawa.

Haka kuma bayan kammala sakadire ne sarki Aminu Ado Bayero ya shiga jami’ar Bayero inda ya karanci fannin jarida.

Bayan ya kammala ne kuma ya shiga makarantar koyon tukin jirgin sama, da ke Birnin Oakland a California da ke kasar Amurka.

Haka kuma ya yi bautar kasa a gidan talabijin na kasa NTA da ke Makurdi.

Sarkin ya fara aiki a matsayin jami’in hulda da jama’a na kamfanin Kabo Air, kafin ya yazama injiniyan cikin jirgi.

Sarautun da ya rike

A shekarar 1990 ne mai martaba sarkin Kano Alhji Ado Bayero ya nada Aminu Ado a matsayin Dan Majen Kano hakimin Dala.

Haka kuma a watan Oktobar wannan shekara ne aka kara daga likkafarsa daga Dan Maje zuwa Dan Buran hakimin Dala.

A shekarar 1992 Alhaji Ado Bayero ya sake daga likkafarsa zuwa Turakin Kano hakimin Dala yayin da a shekarar 2000 aka sake daga likkafarsa zuwa Sarkin Dawakin Tsakar Gida.

A wannan shekara ne kuma ya zama shugaban shirya haye-hayen Dawaki na masarautar Kano.

Haka zalika sarkin Kano Muhammadu Sunusi II ya sake daga likkafarsa daga Sarkin Dawakin Tsakar gida zuwa Wamban Kano a shekarar 2014.

Hakan ce ta sanya a ka sauya masa gari daga Dala zuwa karamar hukumar Birni.

Haka zalika ya samu karin girma zuwa sarkin Bichi, bayan da gwamnan Kano Abudullahi Ganduje ya gididdiba masarautar Kano a shekarar 2019.

Alhaji Aminu Ado Bayero ya zama sarkin Kano a ranar 9 ga watan Maris 2020 bayan da gwamnan Ganduje ya tunbuke sarkin Kano Muhammadu Sunusi II.

Ayyukan sarkin cikin shekara guda

Yana daga cikin ayyukan da sarkin ya gudanar tun bayan zamansa sarki shi ne kai ziyara duk wata masarauta da ke kasar nan domin kara karfafa zumunta.

Haka kuma ya samu damar ganawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari domin tattauna al’amuran da suka shafi ci gaban Kano.

Ya kuma himmatu wajen baiwa gwamnatin Kano hadin kai domin gudanar da yyukanta yadda ya kamata, ba kamar a baya ba da gwamnatin ta ce masarautar na adawa da ita.

Haka zalika tun bayan zamansa sarki ya halarci bikin saukar karatun alkur’ani na makarantu sama da dari a fadin Birnin Kano tare da bude masallatai.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Published

on

Jaafar Jaafar

 

Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.

 

Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

 

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.

 

Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!

 

Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.

 

Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.

 

Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.

 

Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.

 

Allah Ya zaunar da mu lafiya.

Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook. 

 

Continue Reading

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Hausa

Gov. Yusuf Directs Reassigned Commissioners to Handover and Assume Duties by Tuesday, 17th December

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

The Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, has directed all reassigned commissioners to ensure a smooth handover and assumption of duties by Tuesday, 17th December 2024.

Speaking through his spokesperson, Mr. Sanusi Bature Dawakin Tofa, the Governor stated that the cabinet changes will take full effect during the next council meeting on Wednesday, 18th December 2024.

He emphasized the need for the completion of all transition processes before then.

“All commissioners affected by the changes are directed to hand over their responsibilities between Monday, 16th and Tuesday, 17th December 2024,” the statement reads.

The Governor further urged members of the state executive council to redouble their efforts and uphold a strong spirit of teamwork, dedication, and commitment to supporting his administration in serving the good people of Kano State.

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending