Hausa
Dangambo ya zama shugaban gidan Rediyon Vision Kano

Mukhtar Yahya Usman
Hukumar Gudanarwar gidan Rediyon Vision ta amince da nada Abubakar Abdulqadir Dangambo a matsayin sabon shugaban tashar.
Kano Focus ta ruwaito nadin nasa ya biyo bayan murabus da tsohon shugaban tashar Adamu Ladan ya yi da sauran jami’anta guda hudu.
Sauran jami’an da suka yi murabus sun hadar da Turaki Musa mataimaki shugaban tashar, sai Muhammad Garba Malammadori manajan gudanarwa.
Sauran sune Aliyu Gestso shugaban sashin labarai, sai Ahmad Rufa’I Bello mataimakin shugaban sashin labarai.

Sai dai rahotanni na nuni da cewa tsoffin shugabannin sunyi murabus ne, sakamakon takun saka da ke tsakanin su da mamallakan gidan rediyon.
Haka zalika wadanda aka nada a matsayin sabbin shugabanin sun hadar da Abubukar Abdulqadir Dangambo a matsayin shugaba, sai Abubakar Isa Dandago (Yamalash) a matsayin mataimakin shugaba.
Haka kuma an nada Auwal Abdulaziz a matsayin manajan shirye-shirye, sai Isma’il Abba Tangalashi a matsayin shuganan sashin fitar da sakonni daga tashar, sai kuma Abbas Sunusi Gandu shugaban sashin injiniyoyi.
Shi dai Abubakar Abdulkadir Dangambo fitaccen dan jarida ne da ya yi aiki a kafafe yada labarai na ciki da wajen kasar nan.
Ya fara aikin jarida da gidan Rediyo Freedom, da ke nan Kano, har ya kai mukamin Editor, sannan ya kama aiki da sashin Hausa na rediyo Faransa RFI zuwa yazu.
Haka zalika ya yi aiki da gidan rediyon vision a matsayin editor, na wani dan lokaci sanan ya sake komawa aiki da gidan rediyo freedom.
Haka zalika Dangambo ya ci gaba da aiki da jaridar Kano Focus, inda daga nan ne kuma aka nada shi shugaban sashin labarai na gidan rediyon jami’ar Bayero da ke nan Kano.
Sai kuma a yanzu da hukumar gudanarwar vision FM ta ga da cewarsa ta kuma nadashi sabon shugaban tashar.

Hausa
Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Jaafar Jaafar
Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.
Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.
Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!
Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.
Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.
Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.
Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.
Allah Ya zaunar da mu lafiya.
Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook.

Hausa
EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira.
KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.
The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.
The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.
Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.
Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Hausa
Gov. Yusuf Directs Reassigned Commissioners to Handover and Assume Duties by Tuesday, 17th December

Mukhtar Yahya Usman
The Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, has directed all reassigned commissioners to ensure a smooth handover and assumption of duties by Tuesday, 17th December 2024.
Speaking through his spokesperson, Mr. Sanusi Bature Dawakin Tofa, the Governor stated that the cabinet changes will take full effect during the next council meeting on Wednesday, 18th December 2024.
He emphasized the need for the completion of all transition processes before then.
“All commissioners affected by the changes are directed to hand over their responsibilities between Monday, 16th and Tuesday, 17th December 2024,” the statement reads.

The Governor further urged members of the state executive council to redouble their efforts and uphold a strong spirit of teamwork, dedication, and commitment to supporting his administration in serving the good people of Kano State.
