Connect with us

Hausa

Siyasar da za a yi a Kano 2021-2023

Published

on

Malam Ibrahim Shekarau da Engr. Rabiu Musa Kwankwaso

Bello Muhammad Sharada

Tun a bara a watan Disamba na sha alwashin zan yi rubutu da  lakabi na sama. Abubuwa da yawa sun faru har suka kawo wannan jinkiri, YAU ga shi zan sauke wannan nauyin cikin yardar Allah.

A Disambar da ta gabata na kudurce magana ne akan yadda za ta kasance a Kano, bayan na yi nazarin yadda aka gudanar da zabukan ciyamomi na APC. Cikin ikon Allah kuma a jiya da daddare Alhaji Murtala Sule Garo, kwamishinan kananan hukumomin na jihar Kano ya sulale bayan kowa ya watse ya jagoranci ciyamomi na kananan hukumomi 44 ya ziyarci gidan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso domin yi masa ta’aziyya na mutuwar kaninsa shakiki Muhammad Inuwa.

Domin mu sani wadannan ciyamomi sune wanda Hajiya Gwaggo uwar Kanawa da Alhaji Murtala Sule Garo da Alhaji Abdullahi Abbas suka dora akan mulki watanni 11 da suka shude. Haka kuma sune wakilai da ake zato za su yi wa Kwamanda aiki a takarar gwamnan Kano ta 2022-2023 a bisa tsarin Farfesa Hafsat Ganduje, mai dakin gwamna Ganduje.

Wannan ta’aziyya rokon iri ce. Sharar fage ne. Sake lissafi ne. Ni haka na fassara ta. Abin da na fahimta an tara ‘yan tamore, masu yin siyasa bukata, masu yin siyasar kwadayi. Rakuma da akala.

Sai dai irin wannan yanayin a gurina abin farin ciki ne Kwankwaso ya bada auren ‘yar Shekarau. Abin dadi ne Ganduje ya je har gida ya yi wa Kwankwaso ta’aziyya. Gungun yan Gandujiyya su yi takakkiya gaishe da madugu.

Babban kuma farin ciki shi ne, za a daina fadan siyasa na matasa. Za a sassauta jagaliya a fili da rediyo da New Media. Magoya baya zasu rage tsawo na so da kiyayya. Za a koma kan gundarin siyasar manufa da akida da ‘yanci, a wurgar da tumasancin siyasa da biyan bukata.

A tsawon shekara shida zuwa bakwai na mulkin Baba Ganduje kowa zai ba shi shaidar yana zuwa gaisuwar mutuwa da jana’iza da dubiyar maras lafiya da jaje da shi da matarsa, kuma komai kankantar gudunmawa in ta taso zai bayar.

Ba a taba yin gwamna a Kano da ya samu kuri’ar cin zabe ba irinta Ganduje. Ya samu kuri’ar sama da miliyan daya da rabi a zabensa na 2015. Sannan shi ne kadai da ya yi gwamna karo na biyu tare da goyon bayan kowane tsagin siyasa in banda Kwankwasiyya. Sai da ya shawo kan kowa ya bi shi. Amma ba wani gwamna da ya tara bakin jini da hamayya a Kano kamarsa. A tsawon mulkinsa abu guda biyu ya yi wadanda suka jawo masa son barka. Na farko ya cire Sarkin Kano Halifa Muhammad Sanusi II ya kafa sabbin masarautu guda biyar. Na biyu ya dauki mataki akan Sheikh AbdulJabbar Nasir Kabara.

Sai dai kuma faifan bidiyon da aka yada yana cusa Dala a cikin aljihunsa da dan cikinsa da ya kai shi kara EFCC da shigar matarsa dumu-dumu da karfin ikon da take da shi a kowacce harka ta mulkinsa da sakarwa Murtala Sule Garo da Abdullahi Abbas kowacce sabga ta jam’iyyar APC da dora marasa kwarewa a madafun iko, sannan duk harkar kasuwanci da walwala da tausayi da aikin gwamnati da muwalatin ‘yan siyasa babu wata kulawa. Uwa-uba kuma babu wani mai girma da daraja da dattaku a Kano, kowa banza ne, ga kuma musibar tattalin arziki da tsaro su suka dada dagula shirin gwamna Ganduje.

Kanawa bamu da jiha sama da Kano. Duk balokokon da nake yi da masu irin ra’ayina, muna yi ne, don ta bunkasa, tsarin ya amfani al’umma, kuma dukiyar da aka baiwa Kano a yi amfani da su ta hanya mai kyau.

Ina sha’awar jihar Kano ta zama zakara akan sauran jihohi ta fuskokin rayuwa, ina so a rika buga misali da Kano a cikin alheri, ina son Kano ta zama abin koyi da kwatance a cikin sauran takwarorinta. Muna jin labarin jihohi a duniya kamar Selangor a Malaysia da California a America da Taiwan a China da Madina a Saudi Arabia. Haka muke son a ce Kano a Najeriya.

Idan Allah ya nufa nan da watanni takwas za a fitar da wanda zai gajeka a Kano. Cikin watanni masu zuwa hayaniyar siyasa da karbar madafun iko shi ne zai mamaye komai. A shekara 22 da dawowar mulkin farar hula a wannan jamhuriya, da kai aka yi komai. Ka zarce sittin, yanzu ka haura 70, ka doshi 80,  ka san komai kuma ka ga komai. A  cikin shekara 22 ka nuna kwarewar ka a likimo, kai gwani ne.

Bari mu dan yi ratse, mu waiwaya baya. Bayan faduwar PDP a zaben 2015, an rubuta littafai manya da suka shafi siyasar jam’iyyar PDP da mulkin Goodluck Ebele Jonathan. An yi tsokaci kan sababin da ya kawo faduwar PDP bayan shekara goma sha shida a mulki. Na karanta littafai hudu, da suka hada da Against the run of play na Olusegun Adeniyi 2017 da On A Platter of Gold

na Bolaji Abdullah 2018 da My Transition Hours na Goodluck Ebele Jonathan 2018 da Burden of Service na Mohammed Bello Adoke 2019, in ka cire wanda Jonathan ya rubuta da kansa, kaf dinsu sun dangata rawar da mai dakin Jonathan Madam Patience ta taka ya jawo faduwar GEJ/PDP. Matsalar Ganduje bayan ta ‘yan Kwankwasiyya ta Goggo ita ce ta biyu.

 A bana lissafin siyasar Kano sabo ne fil kuma salone da zai zo ba a san irinsa ba a baya. Za a ga abubuwa na siyasa na daban. Idan lokacin ya kara fadada kada a yi mamaki. An samu juyin bukata da yanayi.

Zabi biyu ne da masu lura da sha’anin siyasar gwamnatin tarayya  a Kano suke da shi. Bukatarsu ita ce su samu kuri’a mai kauri daga Kano kowa ye ma zai zama gwamna ruwansu. Zaben shugaban kasa da majalisun tarayya shi za a fara yi.

Zabin kuwa sune ko dai su saka baki bangaren G7 su karbi ragamar Kano su tankade Ganduje can, as-as haihata-haihata, sannan su lallaba su jawo Kwankwaso a hadu guri guda, ko kuma a  watsawa G7 kasa a ido a tabbatar da duk wani tsari da gwamna Ganduje ya zo da shi.

Menene babbar bukatar Kwankwaso? Yana son zama shugaban kasa ko mataimakin shugaban kasa ko ministan Abuja. Sannan yana son wanda duk zai zama gwamnan Kano daga Kwankwasiyya zai fito. Mecece bukatar Ganduje da Goggo, su dora gwamna da zai rufa musu asiri da kare mutuncinsu in sun bar gidan gwamnati, daya daga cikin ‘ya’yan Ganduje ya samu zababben kujera, shi kansa ko ya zama mataimakin shugaban kasa ko Sanatan Kano ta arewa, matarsa kuma ta zama Sanata daga Jigawa.

Mecece bukatar ‘yan G7 shin Barau I. Jibrin ko Sha’aban Ibrahim Sharada ko Shehu Dalhatu ya zama gwamna? Shekarau ya koma Sanatan Kano ta Tsakiya? Abduwa da Dederi da Jobe su koma kan kujerunsu?. Wannan ba ita ce manufar da ya kamata mu dora tunani na al’umma a kai ba. Yanzu burin da ya zamar mana wajibi shi ne; ceto Kano ta zama ta mutanen Kano, harkokin siyasar Kano su kasance a doron dimokuradiyya da ‘yanci da ci gaba da mutunci da zaman lafiya. Babban aikin da za a sanya a gaba shi ne bukatar yadda za a farfado da Kano ta koma matsayinta na asali har ta  zarce kowa a kasuwanci da ilimi da sana’a da fasaha da sarauta da addini da al’ada da lumana da zaman lafiya. A rinka alfahari da ita a duniya.

Wannan burin ya fi karfin Kwankwaso da Kwankwasiyyarsa. Ya fi karfin Shekarau da Mundubuwarsa, burine na dindindin domin Kanawa da Najeriya.

Bello Muhammad Sharada

Shi ne Sakataren dake kula da walwalar ‘Yan Jam’iyyar APC (State Welfare Secretary) na Jiha tsagen Ahmadu Haruna Zago.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

FG kickstarts construction of Emerging Technologies Institute in Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

As part of significant milestone in the Federal Government of Nigeria’s efforts to secure the socio-economic wellbeing of the future generation, as the ground was opened for commencement of construction of the Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI) under the aegis of the National Agency for Science and Engineering Infrastructure (NASENI), The Presidency.

 

KKANO FOCUS reports that the Executive Vice Chaiman/Chief Executive Officer (EVC/CEO) of NASENI, Mr. Khalil Suleiman Halilu during the Ground-breaking ceremony held at the Bayero University Kano (BUK) New Campus said the new institute sits on 30 hectares of the BUK land to be built, featuring state-of-the-art facilities, including innovation hubs devoted to Artificial Intelligence and other cutting-edge technologies, complemented by reliable power supply. “NASENI will fully build and equip and support the new Institute” said the EVC/CEO.

 

The future of socio-economic development for nations rests on human creativity, innovation and cooperation, Artificial intelligence, robotics amongst others.

 

Halilu said that the establishment of SETI in Nigeria is to rapidly respond to the waves of young people globally revolutionizing world economies with unprecedented emergence of socio-economic frontiers as by-products of innovations and ingenuities of these young minds.

 

“We in NASENI are firm believers in the potential of young Nigerians to be the prime catalysts of the type of transformation that Nigeria requires. And we will do everything within our powers to support them to fulfil this important responsibility”

 

“We are gathered here today to kickstart a project that will transform the lives and careers of future generations of young Nigerians. The Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI), located at the Bayero University Kano (BUK) by NASENI. This is very much in line with our operating principles; what we call our 3Cs: Collaboration, Creation, and Commercialization. These 3Cs are the principles that passionately drive us and guide the work that we do to ensure the industrialization of Nigeria in line with the Renewed Hope agenda of President Bola Ahmed Tinubu.”

 

SETI will produce innovators, technologists, entrepreneurs who will make their mark not just in Nigeria but around the world. “I’m eagerly looking forward to the day, not too long from now, when the Institute’s first set of beneficiaries will astonish the world with what they’re capable of accomplishing. These stories will put not just BUK on the global innovation map, but also Kano State and the entire Nigeria” said Halilu.

 

While carrying out the symbolic foundation laying ceremony of the institute as Special Guest of Honour, the Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, described the project as not only laudable but NASENI’s another way of fast-tracking  the placing of Nigeria on the global map of innovation and industrialization. The minister called the project an “ace project” and a pointer to secure a veritable socio-economic development for the nation.

 

In his goodwill message, the Vice Chancellor of BUK, Professor Sagir Adamu Abbas described the new institute as a vehicle for bringing together the three critical tripods for economic and sustainable development for nations, that is, the government, academia and industry. He described the ground-breaking event as the beginning of Nigeria’s journey in pursuit of sustainable development, massive job creation opportunities for the youths, and that the BUK was delighted to be host to such laudable initiative and momentum.

 

There is also, in addition to SETI, a second NASENI project for BUK is an Agri-preneurship Training Hub, that will be equipped with modern greenhouses, and facilities for Soil-less Farming, and Tissue Culture; occupying 10 hectares of land at the Old Campus. These projects collectively represent what NASENI stands for, that is, building capacity, advancing industrialization, supporting economic growth and prosperity.

 

NASENI appreciates the Government and people of Kano State, and the Vice Chancellor, management and students of Bayero University Kano (BUK), for all the support. Special gratitude goes to the Honourable Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, the Special Guest of Honour.

 

NASENI thanked members of the National Assembly for their support, especially the NASENI oversight Committees in both chambers. And of course, President Bola Ahmed Tinubu, who has given NASENI the opportunity to serve Nigeria through his unwavering demonstration of commitment to the success of the Agency.

Continue Reading

Hausa

Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Published

on

Jaafar Jaafar

 

Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.

 

Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

 

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.

 

Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!

 

Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.

 

Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.

 

Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.

 

Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.

 

Allah Ya zaunar da mu lafiya.

Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook. 

 

Continue Reading

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Trending