Connect with us

Hausa

Idan Malamai ba su fadawa shugabanni gaskiya a munbari ba, a Ina za su fada?

Published

on

Daga Salisu Ismail Kabuga

Ita gaskiya, gaskiya ce in dai gaskiyar ce.

Ya yin da aka tozarta gaskiya, ko kuma sai an zabi wanda za’a gayawa gaskiya, ma’ana sai ma su rauni (Talakawa) za’a fadawa gaskiya ba bu shakka an tozartar da gaskiya.

Me ce ce gaskiya kuma a ina za’a fadi Gaskiya?

A takaice Gaskiya, Nasiha ce, wadda ake fadawa mutum/mutane cikin zance ko a wa’azance kamar yadda Malamai ke yi idan za su warware Zare-da-abawa kan wani abu ya yin da suke kan munbarin khudba da ma a kowanne zarafi da suka samu na fede gaskiya.

Irin wannnan muhimmin aiki na fadar gaskiya, ana iya yinsa a ko ina matukar akwai zarafin yin hakan. Kuma gaskiya ta kowa ce. Ma’ana ana iya gayawa kowa gaskiya tunda dai kamar yadda nace a takaice gaskiya Nasiha ce, Ana iya yiwa Shugabanni/Masu mulki masu kudi da Malam Talaka.

Me ye aibu idan an fadi gaskiya?

Matukar gaskiya gaskiyar ce babu wani aibu ga dukkannin bangarori biyu, wato ga wanda ya fadi gaskiya da kuma wanda aka fadawa gaskiyar,  Amma kuma ita gaskiya daci gare ta. Domin ina iya tunawa yadda a wake, Marigayi Sa’adu Zungur ke fadi.

Muddun mutum ko mai wa’azi akan gaskiya yake magana, to kuwa komai fadin gaskiyar ya jawo ta biya, cewar Sa’adu Zungur cikin wakensa.

Yadda malamai a dukkannin sassa suka dada zage damara wajen tunasar da Shugabanni halin da kasa ke ciki na rashin tsaro da kuncin rayuwa da ake ciki a yanzu abin a yaba ne, domin duk Dan’Adam kasasshe ne a koda yaushe yana bukatar a tunasar dashi game da yin abinda ya kamata, kuma ina kyautatawa Malaman nan zaton cewa sunayi ne domin neman gyara.

A ce a wayi gari ana yiwa malamai barazanar raba su da wurare ko munbarorin wa’azinsu domin kawai suna isar da nasiha ga shugabanni kai tsaye daga inda suke da ikon aikewa da sako/wa’azi, yin hakan tamkar komawa zamanin jahiliyya ne.

Ma su cewa, Malamai ba za su yiwa shugabanni Nasiha ko jan hankalinsu akan munbarin karatu/Khudba ba, to a ina kuke so suyi ?

Shin kuna zaton duk wanda nasiha bata yi masa dadi daga munbari ba zayi yi masa dadin ji idan gaka-ga-shi a fadarsa?

Shin ko kuma kuna ganin cewa su wadanda ke kewaye da shugabanni da kuma Yan sa kai wato yan jagaliyar dake kewaye da shugabannin zasu bar Malami ya samu ganin shi (shugaban) cikin karamci, domin ni dai a iya sani na a halin da ake ciki ganin shugabanni musamman na siyasa ba sauki bare shi ba a irin wannan yanayi da ‘yan bani na iya ke kewaye da fadar masu mulki domin kwadayin wani abu.

Haka kuma ina kuka kai tunanin da mafi yawan mutane suke yi cewa, akasarin wadan da shugabanni ke rufe kofa dasu, sunje karbar nasu kason ne musamman idan aka ga Malami ne ?

A tambayi duk wani shugaba cewa ya yake ji idan akace ga shi can Malam wane akan munbarin karatu/khudbar sa ya na fahimtar da jama’a game da wani abin alkhairi da shugaban yayi ko kuma ma ace gashi can yanayi masa addu’a tare da dalibansa ?

Idan har yin hakan ba ketare hakkin iyakar malunta bane, To ta yaya yin wa’azi gare shi akan ya gyara wani abu da yake damun Jama’a akan munbarin da ada aka yabeshi zai zama kuskure? Kuma idan har yabon da Malamai kewa shugabanni akan munbari yayin da sukayi abin yabo bai zama siyasa ba ta yaya gaya musu cewa su gyara ya zama siyasa ?

Dogaro da wannan nazari nake ganin, a ka’idance dama kamata yayi ace Malamai su dinga fadin gaskiya ko wacce iri yayin da suke kan munbarin karatu/khudba domin gaskiya ta kowa ce, ala basshi idan hali ya basu dama wataran sun rabauta da ganin shugaban da suka aikawa da sakon a baya ta kan munbari to sai ku ji tsoron Allah su karasa aikin su na fadin gaskiya gaba-da-gaba kamar yadda ake yiwa dalibai.

A gayawa Duk wani Shugaba dake ci ko Yan kanzagin sa, Shin basu san cewa su MALAMAI sune magada Annabawa ba?

Shin dama akwai abinda addini baiyi magana akan sa ba? Ko kuma ya ware cewa ba za’ayi magana akansa ba ?

Babban aikin Malamai shine shiryadda Al’umma wajen yin dik wani abu dai-dai (politics inclusive), yadda Allah ya ke so da kuma yadda rayuwar Al’umma zata inganta a duniya, kuma idan akace Al’umma ba ana nufin Talaka ba kawai, harda Shugabanni a kowanne mataki.

Idan har Malamai ba za su gayawa Gwamnati da shugabanni inda suka gaza ba ko kuma abinda ya zama matsalar Jama’a, to waye ya fisu wanda zai gayawa shugabannin indai har abinda ake tunasar dasu gaskiya ne?

Muyi hattara Jama’a !

Kudurce jin haushin Malamai a zuci kawai kan iya hana mutum cikawa da imani domin alamune na munafunci, ballantana yinkurin hana Malamai isar da sakon ayi dai-dai wanda aiki ne da Allah ya daura musu saboda sune masu shiryarwa tun da dai a yanzu babu Annabawa.

Gujewa Malamai ko korarsu daga Munbarin wa’azantarwa ko shakka babu aikine irin na Ashararai wadan da suka sanya duniya a gaba, kuma irin wadan nan mutane da yan kanzaginsu da ace a lokacin Annabawa suka zo wallahi irin sune zaka ga suna futo na futo da Annabawan ko ma su kore su daga gari.

Yana daga cikin alamun rashin rabo da tabewa, ka ga mutum ya futo karara yana fada da gaskiya ko kuma yana kare karya da kuma jin haushin duk abinda Malamai ke fada na gaskiya.

Ko wanne musulmi wakilin Allah ne a bayan kasa, kuma rayuwa bata wanzuwa sai kowannen mu ya amsa tare da isar da wakilcin dake kansa da hanyar fadin gaskiya da aiki da ita, domin Allah ne da kansa ya umarci masu Imani dasu kawarda mummunan abu da hannayen su, ko da bakunan su (wa’azi) ko kuma su kyamaci abin a zuciyoyinsu wanda shine mafi raunin Imani.

Babu shakka, halin da Al’ummar Nigeria ke ciki a yanzu na kuncin rayuwa da rashin tsaro wanda ya haifar mana da zullumi da furgici a birane da kauyuka, A yanzu ne ya kamata kowannen mu ya tashi wajen yin abinda zai iya. Ma’ana Shugabanni nayi, Malamai nayi talakawa ma nayi.

Hakika abin takaici ne matuka ace a irin wannan lokaci da kusan kowanne Dannajeriya, masu karfi da raunana, wadanda ke cikin rigar mulki da wadan da ake shugabanta ke cikin rashin tabbaci saboda ba wanda ya tsira, Amma ace wai a samu wasu daga cikin jama’a suna fushi da yadda Malamai ke gayawa gwamnati gaskiya a munbarin su harma ta kai ga dakatar da wasu ko korarsu da sauya su da wanda zaiyi akasin abinda wanda aka kora yayi.

Shin waima tsakanin fushin Allah dana shugaba idan har ba akan dai-dai yake ba, wanne ne abin tsoro? Kowanne Mai imani ya amsawa kansa.

Wannan na a matsayin irin gudummawar da zan iya bayarwa a matsayina na Dan-kasa da kundun mulkin Nigeria ya sahalewa tofa albarkacin bakinsa kuma banyi wannan rubutu da nufin gusgunawa kowa da kowanne bangare ba sai domin fatan ganin Kasa ta (Nigeria) ta samu zaman lafiya da bunkasar arziki ga kowanne Dan-kasa.

Allah ya fudda Kasa ta daga halin da take ciki a yanzu na rashin tsaro da furgici a dukkanin garuruwan Arewacin Nigeria dama sauran sassa na kasar nan dama duniya baki daya. Barka da Azumi !

Cmrd, Salisu Ismail Kabuga

Dan-jarida daga Kano

mallamkabuga@gmail.com

08052529040

4th, April, 2022/3rd, Ramadan, 1443 AH

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

FG kickstarts construction of Emerging Technologies Institute in Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

As part of significant milestone in the Federal Government of Nigeria’s efforts to secure the socio-economic wellbeing of the future generation, as the ground was opened for commencement of construction of the Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI) under the aegis of the National Agency for Science and Engineering Infrastructure (NASENI), The Presidency.

 

KKANO FOCUS reports that the Executive Vice Chaiman/Chief Executive Officer (EVC/CEO) of NASENI, Mr. Khalil Suleiman Halilu during the Ground-breaking ceremony held at the Bayero University Kano (BUK) New Campus said the new institute sits on 30 hectares of the BUK land to be built, featuring state-of-the-art facilities, including innovation hubs devoted to Artificial Intelligence and other cutting-edge technologies, complemented by reliable power supply. “NASENI will fully build and equip and support the new Institute” said the EVC/CEO.

 

The future of socio-economic development for nations rests on human creativity, innovation and cooperation, Artificial intelligence, robotics amongst others.

 

Halilu said that the establishment of SETI in Nigeria is to rapidly respond to the waves of young people globally revolutionizing world economies with unprecedented emergence of socio-economic frontiers as by-products of innovations and ingenuities of these young minds.

 

“We in NASENI are firm believers in the potential of young Nigerians to be the prime catalysts of the type of transformation that Nigeria requires. And we will do everything within our powers to support them to fulfil this important responsibility”

 

“We are gathered here today to kickstart a project that will transform the lives and careers of future generations of young Nigerians. The Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI), located at the Bayero University Kano (BUK) by NASENI. This is very much in line with our operating principles; what we call our 3Cs: Collaboration, Creation, and Commercialization. These 3Cs are the principles that passionately drive us and guide the work that we do to ensure the industrialization of Nigeria in line with the Renewed Hope agenda of President Bola Ahmed Tinubu.”

 

SETI will produce innovators, technologists, entrepreneurs who will make their mark not just in Nigeria but around the world. “I’m eagerly looking forward to the day, not too long from now, when the Institute’s first set of beneficiaries will astonish the world with what they’re capable of accomplishing. These stories will put not just BUK on the global innovation map, but also Kano State and the entire Nigeria” said Halilu.

 

While carrying out the symbolic foundation laying ceremony of the institute as Special Guest of Honour, the Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, described the project as not only laudable but NASENI’s another way of fast-tracking  the placing of Nigeria on the global map of innovation and industrialization. The minister called the project an “ace project” and a pointer to secure a veritable socio-economic development for the nation.

 

In his goodwill message, the Vice Chancellor of BUK, Professor Sagir Adamu Abbas described the new institute as a vehicle for bringing together the three critical tripods for economic and sustainable development for nations, that is, the government, academia and industry. He described the ground-breaking event as the beginning of Nigeria’s journey in pursuit of sustainable development, massive job creation opportunities for the youths, and that the BUK was delighted to be host to such laudable initiative and momentum.

 

There is also, in addition to SETI, a second NASENI project for BUK is an Agri-preneurship Training Hub, that will be equipped with modern greenhouses, and facilities for Soil-less Farming, and Tissue Culture; occupying 10 hectares of land at the Old Campus. These projects collectively represent what NASENI stands for, that is, building capacity, advancing industrialization, supporting economic growth and prosperity.

 

NASENI appreciates the Government and people of Kano State, and the Vice Chancellor, management and students of Bayero University Kano (BUK), for all the support. Special gratitude goes to the Honourable Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, the Special Guest of Honour.

 

NASENI thanked members of the National Assembly for their support, especially the NASENI oversight Committees in both chambers. And of course, President Bola Ahmed Tinubu, who has given NASENI the opportunity to serve Nigeria through his unwavering demonstration of commitment to the success of the Agency.

Continue Reading

Hausa

Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Published

on

Jaafar Jaafar

 

Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.

 

Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

 

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.

 

Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!

 

Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.

 

Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.

 

Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.

 

Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.

 

Allah Ya zaunar da mu lafiya.

Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook. 

 

Continue Reading

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Trending