Connect with us

Hausa

ADP: Zan kawo karshen matsalolin al’ummar Jigawa-Ibrahim Sabo

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

Jam’iyyarADP mai alamar littafi ta tsayar da Alhaji Ibrahim Sulaiman Sabo, a matsayin ɗan takarar gwamna a jihar Jigawa.

Wannan na zuwa ne biyo bayan taron ƙaddamar da takarar tasa, wanda aka gudanar a Alhamis ɗinnan, a helkwatar jam’iyyar dake Dutse babban birnin jihar Jigawa.

Jam’iyyar ta zabi Sabo ne ta hanyar masalaha, inda delegate 16 suka amince da zabin.

Da yake jawabi jim kaɗan bayan ayyana takarar tasa, Alhaji Sabo, wanda haifaffen ƙaramar hukumar Taura ne, yace ya shirya tsaf domin ceto al’ummar Jigawa daga ƙangin da manyan jam’iyyun kasarnan na APC da PDP suka jefasu.

Yace sabuwar dokar zabe da gwamnatin APC ta kawo, ta basu cikkaken gwarin gwiwar samun nasara.

“Lokacin PDP, Jonathan ne ke kan mulki, da Allah ya ƙaddara zuwan ƙarshensa, sai ya kawo Card Reader, wanda shine yayi silar faduwarsa. To itama gwamnatin APC da ta kawo dokar zabe, matukar za’abi ƙa’ida, to ta kada kanta.”

Alhaji Sabo ya ƙara da cewa idan suka kafa gwamnati, zasu baiwa bangaren noma fifiko, zuwa fannin lafiya da ilimi da kuma tattalin arziki.

“Bangaren noma, ina tabbatar maka cewa mudai nan a Arewa, mun rike noma, kuma rabon taki da ake, nima manomi ne amma ban taba samu ba, wannan ba ƙa’ida bace. Kamata yayi a tura wakilai ko ina, a gano gonarka hekta nawa ce, kuma buhu nawa ne zai isheka.”

“Na biyu bangaren lafiya, zan tabbatar cewa in Allah ya yarda, mutum yayi haɗari ya karye ko wani abu ya faru, ba zamu bari ya zauna babu kulawar lafiya ba, har yazo ya mutu.” Inji Alhaji Sabo.

Ya kara da cewa “idan kaba mutum wadataccen abinci da lafiya da ilimi ka gama masa komai.”

Tun daga 6 ga watan Yunin da muke ciki ne jam’iyyar ta ADP ta fitar da yan takarar majalisar jiha 30 ta hanyar masalaha, sannan a 7 ga wata, ta zabi yan takarar majalisar wakilai ta tarayya 11, har ila yau ta kaddamar da masu takarar Sanata gida 3, dukkaninsu ta hanyar masalaha.

Shugaban jam’iyyar na jihar Jigawa, Comrade Bua Abdul Azeez, yace sun zabi fitar da yan takarar ta hanyar masalaha ce bisa amincewar yayan jam’iyyar.

Ya bayyana kwarin gwiwar cewa duk da jam’iyyar tasu ƙarama ce, zatayi nasara, kasancewar dukkanin manyan jam’iyyun sun gaza.

An gudanar da taron ƙaddamar da takarar ce gaban idanun wakilan hukumar zabe INEC, da jami’an yan sanda.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Hausa

Gov. Yusuf Directs Reassigned Commissioners to Handover and Assume Duties by Tuesday, 17th December

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

The Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, has directed all reassigned commissioners to ensure a smooth handover and assumption of duties by Tuesday, 17th December 2024.

Speaking through his spokesperson, Mr. Sanusi Bature Dawakin Tofa, the Governor stated that the cabinet changes will take full effect during the next council meeting on Wednesday, 18th December 2024.

He emphasized the need for the completion of all transition processes before then.

“All commissioners affected by the changes are directed to hand over their responsibilities between Monday, 16th and Tuesday, 17th December 2024,” the statement reads.

The Governor further urged members of the state executive council to redouble their efforts and uphold a strong spirit of teamwork, dedication, and commitment to supporting his administration in serving the good people of Kano State.

Continue Reading

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Trending