Hausa
Kwanaki goman farkon watan Zul-Hajji, ranar Arfah, layyah da bukukuwan Idi

Kwanaki Goman Farkon Watan Zul-Hajji, Ranar Arfah, Layyah Da Bukukuwan Idi
Daga Imam Murtadha Gusau
Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai
Assalamu Alaikum
Yaku bayin Allah masu girma! Ku sani, daga cikin muhimman lokutan yin ibada, lokuta masu tsada, masu falala, wadanda Allah Madaukaki ya hore wa bayinsa, akwai kwanaki goman farkon watan Zul-Hajji – wato wata na goma sha biyu a jerin kalandar Musulunci kenan, wadanda Allah Ya fifita su a kan sauran kwanakin shekara. Hakika, Imamul Bazzar ya fitar da Hadisi a cikin Musnad din sa, daga riwayar Jabir (RA), yace: lallai Manzon Allah (SAW) yace:

“Mafifitan kwanakin duniya, sune kwanaki goman farkon watan Zul-Hajji.” [Albani ya inganta Hadisin a cikin Sahihut-Targib Wat-Tarhib]
Kuma sannan Abdullahi Dan Abbas ya ruwaito cewa, Annabi (SAW) yace:
“Babu wani aiki da yafi alheri fiye da wanda aka yi a kwanaki goma na farkon Zul-Hajji.” Sai wadansu Sahabbai suka ce: “Koda jihadi ne a wurin daukaka kalmar Allah?” Sai Annabi (SAW) yace: “Eh koda jihadi ne a wurin daukaka kalmar Allah, sai dai idan mutum ya tafi da kansa da dukiyarsa bai dawo da komai ba.” [Buhari ne ya ruwaito shi]
Wadannan kwanaki goma masu daraja ne, masu girma da falala ne, kuma mafiya soyuwa ne a wurin Allah (SWT). Abdullahi Dan Umar (RA) ya ruwaito cewa, Annabi (SAW) yace:
“Babu wasu ranaku da suke da girma kuma mafi soyuwa a wurin Allah fiye da wadannan kwanaki goma na farko Zul-Hajji, don haka ku yawaita tahlili da takbiri da tahmidi a cikinsu.” [Musnad Imam Ahmad, kuma Sheikh Ahmad Shakir ya inganta shi]
Daga cikin darajojin da wadannan kwanaki goma suke da su akwai cewa:
1. Mun sani, Allah Yana yin rantsuwa da wani abu domin Ya nuna muhimmancinsa da girmansa da matsayinsa a wurin sa, kuma Allah Yayi rantsuwa da wadannan kwanaki goma a cikin Alkur’ani Mai girma, a inda yace:
“Ina rantsuwa da alfijir. Da darare goma.” [Al-kur’ani, 89:1-2]
Malamai magabata da suka hada da Abdullahi Dan Abbas (RA) sun ce wadannan darare goma da aka ambata a cikin wadannan ayoyi na Alkur’ani, su ne kwanaki goma na farkon Zul-Hajji.
2. Annabi (SAW) yace wadannan kwanaki goma sune ranaku mafiya alheri a shekara, kamar yadda muka ambata a Hadisi na sama.
3. Su ne ranaku mafiya alheri na yawaita ambaton Allah (wato Zikiri), kamar yadda Hadisin da ya gabata ya nuna.
4. Wadannan kwanaki goma a cikin su ne ake da rana mai kima da daraja, wato ranar Arfah, ranar 9 ga Zul-Hajji, wanda a cikinta ne (ranar Arfah) Allah Ya kammala wannan addini, kuma ya cika wa bayinsa ni’imarsa. A ranar Arfah ne shaidan, iblis la’ananne yake bakin ciki, yake jin haushi, yake kuka da shiga damuwa, saboda rana ce da Allah yake ‘yanta bayinsa daga azaba, kuma rana ce da Allah yake gafartawa dukkanin bayinsa. Kuma yin azumi a ranar Arfah ga wanda baya wurin aikin Hajji, yana kankare kananan zunuban shekarar da ta gabata da shekarar da ake ciki, (manyan zunubai kuma suna bukatar tuba da mayar da hakki ga mai shi).
5. Wadannan kwanaki goma na farkon Zul-Hajji, a cikin su ne ake da ranar “Hajji Mafi girma” wato ranar Idin Layyah (wato 10 ga Zul-Hajji kenan). Kuma kamar yadda muka sani, wannan rana ita ce rana mafi girma a daukacin shekara.
Don haka yaku ‘yan uwana masu daraja, kuyi kokari ku yawaita karatun Alkur’ani a cikinsu, kuyi sallolin nafilah da kiyamul Laili da sadaka da kyauta da alkhairi da yada ilimi da tuba da neman gafarar Allah. Ku yawaita neman gafarar Allah, ta fadin Astagfirullah, kuyi azumi da jikinku, ma’ana ku kaurace wa haram ko fadin haram ko sauraren haram ko cin haram da sauransu. Kuma ku yawaita yin addu’o’in alheri, da addu’o’in zaman lafiya, musamman ga kasar mu Najeriya, da al’ummar Musulmin Najeriya, da al’ummar Musulmin duniya baki daya.
Yaku ‘yan uwana maza da mata! Lallai ya zama tilas dukkanin mu muyi gaggawa wurin ribatar wadannan kwanaki kafin lokaci ya kure muna.
Bayan wannan, yaku bayin Allah! Ku sani, a yau, babu wani aikin da yafi hada dukan Musulmi, matasa da dattawa, maza da mata, bakake da farare, kuma yake kawo farin ciki a fuskar kowa da kowa, kamar bukin ranar Idi da ibadar Layyah. Layyah ibada ce ta sadaukarwa, ta hanyar yanka dabbobi domin neman yardar Allah. Ana yin ta ne domin tunawa da wani muhimmin abin tarihi da ya auku a lokacin da Allah Ya umarci Annabi Ibrahim (AS) da yayi layyah da dan sa Annabi Isma’il (AS). A lokacin da yake shirin aiwatar da umarnin Allah, sai Allah Ya musanya masa da rago mai girma, ya fanshi Annabi Isma’il da shi, wanda Annabi Ibrahim (AS) ya yanka. Lallai Annabi Ibrahim (AS) da dan sa Annabi Isma’il, sunci jarrabawa, domin ya shirya don ya yanka dan sa saboda bin umarnin Allah, shi kuma dan ya amince a yanka shi saboda mika wuya ga umurnin Mahalicci!
Yaku Abokaina masu girma, yanzu gashi ayau, muna jin wahala kwarai ko, wurin yin layyah da dabba (ta hanyar amfani da kudinmu) domin bin umarnin Allah? To ina ace ‘ya ‘yan mu ne Allah yace mu yanka? A gaskiya bai kamata ni da ku mu kasa cin wannan jarrabawa ba. Don haka duk wanda yake da hali don Allah yayi layyah, a madadinsa da iyalinsa.
’Yaku ‘yan uwana maza da mata! Ku sani, za’a iya yanka Layyah a kowane lokaci bayan Sallar Idi har zuwa faduwar rana ta uku a bayan ranar Idin. Wannan na nufin wuni hudu (wunin Idi da karin wuni uku na ayyamut-tashriq). Kamar yadda Imamu Shafi’i ya nuna. Amma a fahimtar sauran manyan malamai: Abu Hanifah da Malik da Ahmad, sun ce ana yin layyah ce a cikin wuni uku. A fara da ranar Idi a kare a wuni na biyu bayan wunin Idi, lokacin faduwar rana.
Ana iya yanka Layyah da rana ko da dare, matukar dai a cikin wadannan ranaku ne, amma yin ta da wuri (jim kadan bayan Sallar Idi) shi yafi.
Sannan Sunnar Layyah ita ce a raba naman kashi uku, kuma ba tilas ba ne a raba daidai-wa-daida. daya a raba wa talakawa da mabukata, dayan a bar wa iyali da makwabta da dangi da abokai, dayan kuma ka yi yadda ka so da shi.
Layyah Sunnah ce mai karfi a kan kowane Musulmi mai hali. Wannan shine ra’ayin akasarin malamai. Amma a wurin wadansu malaman sun ce wajiba ce a kan Musulmin da yake da halin yin ta. Kuma tana daya daga cikin kyawawan ayyuka a Musulunci kamar yadda A’isha (RA) ta ruwaito daga Annabi (SAW) cewa:
“Dan Adam bai taba yin wani aiki a ranar Layyah ba wanda yafi soyuwa a wurin Allah, kamar zubar da jinin dabba (wato yanka dabbar Layyah).”
Kuma galibin malamai sun tafi a kan cewa, yanka Layyah shi yafi alheri a kan yin sadaka da kwatankwacin kudin abin yankar.
Yaku ’yan uwana! Ku sani, ana yin Layyah ne da dabbobin gida, dabbobin ni’ima, wato: shanu da rakuma da tumaki da awaki. Kuma yanka rago/tunkiya da bunsuru/akuya shi yafi a kan sauran dabbobin, saboda Annabi (SAW) bai taba yin Layyah ba face da wadannan dabbobi. Amma ana iya yanka rakuma da shanu lokacin Layyah. Kuma wajibi ne abin yankan ya kasance lafiyayye, kosasshe wanda za’a iya cin naman sa a matsayin ibada ga Allah kamar yadda Allah Yace:
“Kuma wanda ya girmama ibadojin Allah, to lallai ne ita (girmamawar) tana daga ayyukan zukata na takawa (wato tsoron Allah).” [Al-kur’ani,22:32]
Don haka kenan dabbobi marasa lafiya, ko masu aibu basu yin layyah.
Kuma wajibi ne idan rago ne ko tunkiya su haura wata shida kamar yadda Ibn Majah ya ruwaito cewa, sai Jaza’ah za’a yi Layyah da ita. Ga jinsin akuya kuwa wajibi ne ya kai shekara daya. Sannan sa ko saniya shekara biyu, shi kuma rakumi shekara biyar.
Kuma kada ayi Layyah da nakasasshiyar dabba, kamar mai ido daya ko marar lafiya ko gurguwa wadda hakan ya bayyana, ko ramammiya marar mai da nama, kamar yadda Buhari ya ruwaito daga Barra’u Dan Azib (RA), daga Annabi (SAW).
Kuma mafi yawan malamai sun tafi a kan cewa siffofi hudu da aka ambata a Hadisin za’a iya amfani dasu wajen hukunci a kan duk wata nakasa. Don haka duk wata nakasa da ta kai ta, ko tafi ta, to ba za’a yi Layyah da dabbar ba, kamar makauniya ko marar kafa daya.
Kuma ana iya yin Layyah da dabbar da aka dandake, saboda Annabi (SAW) yayi haka. Haka dabbar da aka haifa ba ta da jela/bindi ko wanda take da rabin jelar, amma wadda aka yanke jelarta/bindinta duka ba za’a yi Layyah da ita ba.
Sannan tunkiya ko akuya daya ta wadatar mai gida yayi Layyah da ita ga kansa da iyalansa. Kuma ya halatta mutum bakwai su yanka saniya ko rakumi daya a matsayin layyarsu. Kamar yadda Jabir Dan Abdullahi (RA) ya ruwaito cewa Annabi (SAW) yayi haka a shekarar Sulhun Hudaibiyyah. [Muslim ne ya ruwaito shi]
Kuma mai yin haka zai iya hadawa da iyalinsa a cikin ladan domin a nan daidai yake da mai yanka tunkiya ko akuya.
Kuma bai halatta a yanka Layyah kafin yin Sallar Idi ba, duk wanda ya yanka layyah kafin Idi, to ya sani, ya yanka wa iyalinsa nama sun ci ne kawai, amma bai yi Layyah ba, kamar yadda Annabi (SAW) ya nuna. Kuma idan mutum zai yanka layyar ana so ya ambaci sunan Allah, yace:
“Bismillah, Ya Allah, wannan daga rahamarKa ce kuma dominKa ne.”
Sannan an fi so mutum ya yanka dabbar Layyarsa da hannunsa, idan ba zai iya yin haka ba, to ya halatta ya wakilta wani, kuma ya halarci wurin yankan, sannan ya raba naman kashi uku kamar yadda na ambata a baya. Yaci rubu’i daya shi da iyalinsa, ya bayar da daya rubu’in sadaka, dayan kuma yayi kyauta da shi, kamar yadda Annabi (SAW) ya shaida wa ’yar sa Fatima (RA) cewa:
“Ki kasance a wurin, lokacin da ake yanka dabbar Layyarki. Allah Yana gafarta miki a lokacin digar farko na jininta.” [Baihaki da Abdul Razzak]
• Hikimar shar’anta yin Layyah:
1. Neman kusanci ga Allah ta hanyarta.
2. Raya Sunnar Shugaban Masu Tauhidi, Annabi Ibrahim (AS), wanda Allah Ya umarce shi yayi Layyah da dan sa Annabi Isma’il (AS) sannan daga baya ya musanya shi da rago, Annabi Ibrahim (AS) ya yanka shi a madadin Annabi Isma’il (AS) din.
3. Yalwatawa da kyautata wa iyali a ranar Idi.
4. Sanya jin dadi a tsakanin matalauta da mabukata, ta hanyar ba su sadakar naman Layyah.
5. Yin godiya ga Allah akan yadda ya hore muna dukkan dabbobin ni’ima (wato Bahimatil An’am).
• Abubuwan da wanda yayi niyyar Layyah zai guje musu:
Idan mutum yayi niyyar zai yi Layyah to da zarar watan Zul-Hajji ya kama, ba zai yi aski ko ya yanke farce/kumba/akaifa ba har sai ya yanka abin Layyarsa. Muslim ya ruwaito a cikin Sahihinsa cewa Ummu Salmah (RA) cewa, Annabi (SAW) yace:
“Idan kuka ga jinjirin watan Zul-Hajji, kuma dayanku yana da niyyar yin Layyah, to kada ya aske gashinsa ko ya yanke farcensa.” [Muslim]
Haka kada a biya ladan mai gyaran naman Layyah daga abin Layyar. Domin Aliyu Bin Abi Talib (RA) yace:
“Manzon Allah (SAW) ya umarce ni da in lura da Layyar wani rakumi, in bayar da namansa da fatarsa a matsayin sadaka, kuma kada in bayar da komai daga cikinta ga mahauci a matsayin ladan aikinsa. Yace, “Zan iya ba shi wani abu daga abin da na mallaka.” [Muslim]
Ya ku bayin Allah masu girma! Lallai babu shakka, idan watan Zul-Hajji ya kama, kuma shigowarsa ko ganinsa ya tabbata, shugabannin da Allah ya dora wa alhakin yin sanarwa suka yi sanarwa, kuma dayan ku yana da niyyar yin Layyah, to an hana shi ya rage gashi ko ya aske gashi a jikin sa. Haka kuma an hana shi ya rage farce/kumba/akaifa, ko ya rage wani abu daga cikin fatar jikinsa. Amma ba’a hana mata masu niyyar yin ibadar layyah suyi Kitso ko suyi lalle/kunshi ko sanya turare ba, kamar yadda naji wasu suna fada.
Kuma ya kamata mu sani, wannan hukuncin ya shafi mai niyyar yin layyar ne kawai, ban da matansa da sauran iyalin gidansa. Haka nan hukuncin bai shafi wanda aka sanya shi matsayin mai wakiltar layyar wani ba, koda shine zai yanka. Wannan hukuncin ya shafi mai niyyar layyah ne kawai, ya hada namiji da mace duk daya ne, in ban da maganar kitso da lalle. Wannan kuwa saboda ingantaccen Hadisin uwar Muminai Ummu Salmah (RA) tace:
“Lallai Manzon Allah (SAW) yace: Idan aka ga watan Zul-Hajji, kuma dayan ku yayi niyyar yin Layyah, to ya kame daga aske gashinsa da farcensa.” [Muslim ne ya ruwaito shi]
A wata ruwayar yana cewa: “Kada ya rage wani abu daga gashinsa ko fatarsa.”
Hakika malamai sun tattauna, kuma sun karawa juna sani game da wannan Hadisin. Dan Musayyib yana cewa: Da Rabi’atu Dan Abdurrahman da Imam Ahmad da Imam Is-haq da Dawud da wani bangare na Mabiya Shafi’iyyah sun tafi akan cewa:
“Baya halatta, wato haramun ne ga mai niyyar yin layyah idan watan Zul-Hajji ya kama, ya rage gashi ko farce ko wani abu a fatarsa, har sai ya yanka dabbar layyar sa, saboda Hadisin da yazo a zahiri yana hukunta haka…” [Duba Sahihu Fiqhus-Sunnah wa Adillatuhu, mujalladi na 2, shafi na 375]
Sannan Imamu Malik da Imamu Shafi’i, mabiya shafi’iyyah, sun tafi akan cewa:
“Yin hakan makaruhine, wato ka yanke farce ko ka aske gashi. Hani ne na karhanci wanda aka kyamata, ba haramun bane, saboda Hadisin Nana Aisha (RA)…” [Bukhari da Muslim]
Sannan Majalisar Koli ta kwamitin Malaman Kasar Saudiyyah wato Al-Lajnatid Da’imah…, sun bayar da fatawa cewa:
“An shar’anta wa mai niyyar yin layyah cewa, idan an ga watan Zul-Hajji, kada ya rage wani abu daga jikin fatarsa ko gashinsa ko farcensa, har sai ya yanka abin yankan sa. Saboda Hadisin da Malaman Hadisi guda shida suka ruwaito in ban da Imamul Bukhari, daga Ummu Salmah (RA), tana cewa lallai Manzon Allah (SAW) yace: “Idan anga jinjirin watan Zul-Hajji, kuma dayan ku yana da niyyar yin Layyah, to kada ya rage wani abu daga gashinsa ko farcensa.”
A cikin lafazin da Imam Abi Dawud da Muslim da Nasa’i suka ruwaito yana cewa:
“Wanda yake da abin layyar sa idan watan Zul-Hajji ya kama, kada ya rage wani abu daga gashin jikinsa ko farcensa, har sai ya yanka abin yankan sa.” [Duba Fatawa Al-Lajnatid Da’imah, mujalladi na 11, shafi na 397-398]
Sannan Imam Ibn Hazm (rahimahullah) yana cewa:
“Wanda yake son yayi Layyah, idan aka ga sabon watan Zul-Hajji, to wajibi ne a kan sa kada ya rage wani abu na gashin jikinsa ko farcensa, har sai ya yanka abin yankansa. Amma wanda baya da niyyar yin layyah, wannan hukunci bai hau kansa ba.” [Duba Al-Muhallah na Ibn Hazm]
Sannan Imam Ibn Qudamah (rahimahullah) yana cewa:
“Idan tsayuwar watan Zul-Hajji ya tabbata, to mai niyyar yin Layyah zai kame daga yanke farce da aske gemu idan kuma yayi hakan to sai ya nemi gafarar Allah, babu fansa a kan sa a bisa haduwar Malamai, kuma ya aikata hakan da mantuwa ne ko da gangan.” [Duba littafin Al-Mugni, mujalladi na 9, shafi na 346]
Sannan Imamu Shawkani (rahimahullah) yana cewa:
“Hikimar da ke cikin hani akan rage gashi ko farce ga mai niyyar yin layyah shine, domin ya sami cikakkiyar ladar sa ta layyah, na samun ‘yantawa gaba daya daga wuta zuwa Aljannah, domin kuma yayi koyi da mai yin aikin Hajji cikin Ihrami, an hana shi wadannan abubuwa a lokacin aikin Hajji har sai ya gama jifan farko. To kai ma a nan gida sai aka sa ka kayi hakan don samun ladar ibadah irin ta shi…” [Duba littafin Nailul Autar na Imamu Shawkani, Mujalladi na 5, shafi na 133]
Sannan game da Malaman da suke karyata ko musun wannan Sunnah ta hana yanke farce da aske gashi ga mai niyyar yin Layyah, ina kira da suji tsoron Allah, su daina yin izgilanci da Hadisan Annabi (SAW), su daina batar da al’ummah da sunan bin Mazhaba ko kuma bin wani Malami. Su daina yada irin wannan sabani, domin kaucewa rudani da haifar da rarrabuwa a cikin al’ummah. Suji tsoron Allah, su tabbatar da abinda ya tabbata da ingantattun hujjoji, su daina kore duk wani abu da nassi ya tabbatar da shi, kawai domin son zuciyar su da kuma neman a sansu, ko don girman kai, da kin karbar gaskiya.
Wannan mas’alah ba wata sabuwar mas’alah bace. Malamai magabata nagartattu, masu ikhlasi da tsoron Allah sun yi bayanin ta. Don haka, a yau wani yazo da rana tsaka ya nemi rusa abinda ya tabbata kuma ya inganta a Hadisin Annabi (SAW), kawai don son zuciyar sa, ko don dakusasshen ra’ayin sa, sam wannan ba zai karbu ba a wurin duk wani mai imani, kuma al’ummah ba zasu taba yarda da shi ba. Ina addu’a da rokon Allah ya nuna muna gaskiya ya bamu ikon bin ta, kuma ya nuna muna karya ya bamu ikon guje mata, amin.
A takaice dai jama’ah, layyah ita ce abun da ake yankawa na daga dabbobin ni’ima (wato Bahimatul An’am), kamar yadda bayani ya gabata a baya. Wato rakuma, shanu, awaki da tumaki, a ranar yanka (wato ranar babbar Sallah) da kuma ranakun shanyar nama ko busar da shi (wato ayyamut-tashriq), da niyyar yin ibadar layyah. Sannan a bisa zance mafi inganci daga cikin zantukan Malamai shine, layyah Sunna ce mai karfi ga mai ikon yi (amma wasu malamai suna ganin idan mutum yana da halin yin layyah, to wajibi ce a gare shi).
Kuma lokacin yanka dabbar layyah shine, daga bayan Sallar idi na ranar babbar Sallah har zuwa karshen ranakun busar da nama (wato ranakun 10, 11, 12 da 13 kenan).
Sannan an sunnanta raba naman layyah kashi uku, wato mutum yaci kashi daya da iyalansa, yayi sadaka da kashi daya, kuma yayi kyauta da kashi daya.
Ya ku jama’ah, ku sani, layyah tana da falala mai girman gaske, domin abunda ke cikin ta na lada mai tarin yawa da kuma amfanar da talakawa, da kuma toshe musu hanyar roko domin bukatun su.
Sannan mu sani, ba’a yin layyah ko hadaya da komai sai abinda ya kasance na rakumi matashi mai akalla shekara biyar. Sannan da shanu ko maraki akalla mai shekara biyu. Sannan rago akalla mai watanni shida. Sai taure akalla mai shekara daya.
Sannan game da akuya da rago da taure da tunkiya, ko wannen su yana halatta ne ga mutum daya. Rakumi kuma ga mutane bakwai, sa ko saniya kuma su ma ga mutane bakwai. Kuma ya halatta mutum yayi layyah da akuya ko rakuma ko sa, ga kansa da kuma iyalansa. Kuma ya zama wajibi abunda za’a yi layyah da shi ya kasance mai lafiya, mara aibu ko wata matsala.
Kuma kamar yadda kuka sani, kuma kamar yadda fadar Mai Alfarma Sarkin Musulmi suka sanar, yau muna ranar Asabar, 03 ga watan Zul-Hajji, 1443 AH, wanda yazo daidai da 02/07/2022, kenan daga yau bai wuce saura kwanaki 7 mu shiga babbar Sallah ba (sati daya), idan Allah yasa muna cikin masu yawancin rai.
Ina rokon Allah ya bamu ikon ganin babbar Sallah lafiya, ya bamu hali da ikon sayen dabbar layyah, kuma ya bamu lafiya da zaman lafiya da ci gaba mai dorewa, a kasar mu Najeriya da kuma yankin mu na arewa baki daya.
Ya Allah, muna tawassali da sunayenka tsarkaka, ka tausaya muna, ka karbi tuban mu, ka azurta mu da hakuri, juriya, jajircewa da ikon cin jarabawarka a koda yaushe.
Ya Allah, kayi muna gafara, ka shafe dukkan zunuban mu, don son mu da kaunar mu ga fiyayyen halitta, Annabin rahmah, Muhammad (SAW).
Ina rokon Allah ya kyauta, ya kawo muna mafita ta alkhairi a cikin dukkanin al’amurran mu, amin.
Yaku ‘yan uwana maza da mata! Ina rokon Allah Madaukaki ya amsa min da kuma ku da sauran Musulmin duniya baki daya, kuma Yasa dominSa kadai muke yi. Tsira da amincin Allah su kara tabbata ga Annabi Muhammad (SAW) da iyalansa da Sahabbansa. Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai.
Ya Allah! Ka taimake mu wurin rayuwa bisa koyarwar Alkur’ani da Sunnah. Ya Allah Ka nuna mana gaskiya kuma Ka bamu ikon bin ta, kuma Ka nuna mana karya Ka bamu ikon guje mata.
Ya Allah! Ka shiryar da mu, Ka kare mu daga ayyukan jahilci da barna. Ka kare mu daga gazawarmu. Ka sanya karshen ayyukanmu su kasance mafi alherinsu da dacewarsu. Kuma Ka gafarta mana Ya Ubangiji.
Yaku ’yan uwana! Ku sani, duk abin da na fada mai kyau a wannan jawabi na yau, ni’ima ce da falala daga Allah Madaukaki, kuma duk wani kuskure daga gare ni ne, kuma ina neman tsarin Allah daga bayar da muguwar shawara, da kuma daga dukkan barna da fitina. Kuma ina rokon Allah gafara idan na ketare iyaka a cikin duk abin da na ce ko na aikata.
Godiya ta tabbata ga Allah, Tsira da amincin Allah su kara tabbata ga Manzon Allah da alayensa da Sahabbansa.
Ina mai kammala wannan jawabi nawa, ina mai rokon Allah Madaukaki Ya gafarta mana zunubanmu. Ku nemi gafararSa, Lallai Shi (Allah) Mai gafara ne Mai jin kai.
Daga karshe, yaku bayin Allah! Muna neman taimakon ku matuka, domin ci gaba da gudanar da ayukkan mu na da’awa da yada ilimi da karantarwa da kula da marayun da suke karkashin kulawar mu. Ku sani, wadannan marayu suna bukatar cin naman layyah kamar yadda ‘ya ‘yan mu suke bukata. Ku tallafa masu, kuma sai Allah ya tallafawa ‘ya ‘yan ku a bayan ku. Ku taimaka, kuma sai Allah ya taimake ku a cikin dukkanin abun da kuka sa a gaba. Kun san cewa gaskiyar magana, duk abubuwan da muke yi wallahi makudan kudade muke kashewa wurin aiwatar da shi, domin ayau, babu abunda ake yi kyauta, ba da kudi ba. Don Allah ku taimaka Fisabilillah!
Muna godiya, Allah ya biya ku da mafificin alkhairi duniya da lahira, amin.
Ga lambar Account kamar haka:
Account no. – 0048647196
Account name – Murtala Muhammed
GTBank
Wassalamu alaikum,
Dan uwanku:
Imam Murtadha Muhammad Gusau, Babban Limamin Masallacin Juma’ah na Nagazi-Uvete, da Masallacin marigayi Alhaji Abdurrahman Okene, da suke garin Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za a iya tuntubar Imam ta lambar tarho kamar haka: +2348038289761 ko email: gusaumurtada@gmail.

Hausa
FG kickstarts construction of Emerging Technologies Institute in Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
As part of significant milestone in the Federal Government of Nigeria’s efforts to secure the socio-economic wellbeing of the future generation, as the ground was opened for commencement of construction of the Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI) under the aegis of the National Agency for Science and Engineering Infrastructure (NASENI), The Presidency.
KKANO FOCUS reports that the Executive Vice Chaiman/Chief Executive Officer (EVC/CEO) of NASENI, Mr. Khalil Suleiman Halilu during the Ground-breaking ceremony held at the Bayero University Kano (BUK) New Campus said the new institute sits on 30 hectares of the BUK land to be built, featuring state-of-the-art facilities, including innovation hubs devoted to Artificial Intelligence and other cutting-edge technologies, complemented by reliable power supply. “NASENI will fully build and equip and support the new Institute” said the EVC/CEO.

The future of socio-economic development for nations rests on human creativity, innovation and cooperation, Artificial intelligence, robotics amongst others.
Halilu said that the establishment of SETI in Nigeria is to rapidly respond to the waves of young people globally revolutionizing world economies with unprecedented emergence of socio-economic frontiers as by-products of innovations and ingenuities of these young minds.
“We in NASENI are firm believers in the potential of young Nigerians to be the prime catalysts of the type of transformation that Nigeria requires. And we will do everything within our powers to support them to fulfil this important responsibility”
“We are gathered here today to kickstart a project that will transform the lives and careers of future generations of young Nigerians. The Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI), located at the Bayero University Kano (BUK) by NASENI. This is very much in line with our operating principles; what we call our 3Cs: Collaboration, Creation, and Commercialization. These 3Cs are the principles that passionately drive us and guide the work that we do to ensure the industrialization of Nigeria in line with the Renewed Hope agenda of President Bola Ahmed Tinubu.”
SETI will produce innovators, technologists, entrepreneurs who will make their mark not just in Nigeria but around the world. “I’m eagerly looking forward to the day, not too long from now, when the Institute’s first set of beneficiaries will astonish the world with what they’re capable of accomplishing. These stories will put not just BUK on the global innovation map, but also Kano State and the entire Nigeria” said Halilu.
While carrying out the symbolic foundation laying ceremony of the institute as Special Guest of Honour, the Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, described the project as not only laudable but NASENI’s another way of fast-tracking the placing of Nigeria on the global map of innovation and industrialization. The minister called the project an “ace project” and a pointer to secure a veritable socio-economic development for the nation.
In his goodwill message, the Vice Chancellor of BUK, Professor Sagir Adamu Abbas described the new institute as a vehicle for bringing together the three critical tripods for economic and sustainable development for nations, that is, the government, academia and industry. He described the ground-breaking event as the beginning of Nigeria’s journey in pursuit of sustainable development, massive job creation opportunities for the youths, and that the BUK was delighted to be host to such laudable initiative and momentum.
There is also, in addition to SETI, a second NASENI project for BUK is an Agri-preneurship Training Hub, that will be equipped with modern greenhouses, and facilities for Soil-less Farming, and Tissue Culture; occupying 10 hectares of land at the Old Campus. These projects collectively represent what NASENI stands for, that is, building capacity, advancing industrialization, supporting economic growth and prosperity.
NASENI appreciates the Government and people of Kano State, and the Vice Chancellor, management and students of Bayero University Kano (BUK), for all the support. Special gratitude goes to the Honourable Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, the Special Guest of Honour.
NASENI thanked members of the National Assembly for their support, especially the NASENI oversight Committees in both chambers. And of course, President Bola Ahmed Tinubu, who has given NASENI the opportunity to serve Nigeria through his unwavering demonstration of commitment to the success of the Agency.

Hausa
Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Jaafar Jaafar
Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.
Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.
Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!
Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.
Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.
Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.
Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.
Allah Ya zaunar da mu lafiya.
Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook.

Hausa
EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira.
KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.
The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.
The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.
Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.
Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.
