Connect with us

KANUN LABARAI

Masarautar Rano ta dakadar da dagatai biyu da suka sace tallafin Korona

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

Masarautar Rano da ke jihar Kano ta dakatar da Dagatai guda biyu sakamakon zarginsu da ɓoye kayan tallafin korona da gwamnati ta bayar a rabawa talakawa.

Kano Focus ta ruwaito Chiroman Rano kuma hakimin Rano Alhaji Manniru Tafida Abubakar ILa ne ya dakatar da dagatan biyu, bisa umarnin mai martaba Sarkin Rano Alhaji Muhammadu Kabiru Inuwa.

Dagatan da su ka haɗa da Umar Yusuf, wanda shi ne dagacin Zurgu da kuma Kamilu Zambur da shi kuma ya ke a matsayin Dagacin Zambur, ana zarginsu da ƙin rabawa talakawansu kayayyakin abinci wanda gwamnati ta bayar domin ragewa al’umma radadin rayuwa.

Tuni dai aka aike da wakilci zuwa ƙasar dagatan da abin ya shafa.

KWARONA: Ana Zargin kwamandan Hisbah da sace kayan tallafi

Hisbah ta dakatar da kwamandan da ake zarigi da sace tallafin Korona

Ra’ayi:Yanayin sanyi ke samu sanya takunkumin fuska a Kano ba cutar Korona ba

Idan za a iya tunawa dai makwanni biyu da su ka gabata aka samu rahoton kwamandan hisbah na karamar hukumar Dala Siyudi Muhammad Hassan, da zargin sace tallafin kwarona da karamar Hukumar Dala ta baiwa jami’an hisbar.

Haka zalika a cikin watan Oktoba ma sai da hukumar yaki da cin hanci da rashawa da kuma sauraron korafe korafe ta jihar Kano, ta tsare shugaban karamar hukumar Kumbotso Alhaji Kabiru Ado Panshekara, bisa tuhumar sa da yin amfani da karfin kujerarsa wajen karkatar da tallafin kayan masarufin gwamnati na ragewa jama’a radadin dokar hana su fita saboda annobar coronavirus.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending