Connect with us

KANUN LABARAI

Jam’iyyar APC a Kano na yunkurin hallakani-Saha’aban Sharada

Published

on

Aminu Abdullahi

Dan Majalissar tarayya mai wakiltar karamar hukumar birni Sha’aban Ibrahim Sharada ya zargi jam’iyyar APC ta jihar Kano da bada umarnin hallakashi.

Sha’aban Sharada ya ce jam’iyyar ta bada umarnin ne yayin zaben fidda gwani na ‘yan takarar shugabancin kujerar shugabancin karamar Hukumar ta birni.

Kano Focus ta rawaito dan majalisar ya bayyana hakanne ya yin hirarsa da Freedom Radiyo ranar Lahadi.

Ya ce shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar birni Malam Sani Fata da makarrabansa sun yi amfani da sojojin haya amatsayin shugabanin mazabu, da su ne su kayi dangwale ba ainihin shugabanin jam’iyyar na mazabu ba.

Ya kuma ce akwai wasu manya da ke tare da gwamnati su biyu a karamar da suka turo da yan daba domin tarwatsa taron, kuma su hallakashi.

A cewarsa hakan ta sanya ba shiri shi da magoya bayansa suka bar wurin da ake gudanar da zaben

Da gangan aka raba kan jam’iyya

Sha’aban Sharada ya ce da gangan aka bar jam’iyyar APC ta rabu gida biyu a karamar hukumar Birnin zuwa bangaren dake samun goyan bayan gwamnati da kuma bangaren sa dake samun temako daga Allah.

“Kamar yadda yake idan aka gaza samun sulhu tsakanin ‘yan takara ana gudanar da zaben fidda gwani to a karamar hukumar birni ma haka ce ta kasance.

“Bangaren gwamnati sun bada nasu dan takarar Hafizu Alfindiki muma bangaren mu mun tsaida Murtala Sunusi Dandawaki,” a cewar sa.

Malam Sharada ya sun biya kudin form na takarar shugabancin karamar hukumar dana kansiloli goma sha uku naira miliyan daya da dubu dari takwas.

Amma jam’iyyar taki basu fom din har saida suka rubuta takadar korafi zuwa ga shugabancin jam’iyyar na jiha kana daga baya ana sauran kwana daya a gudanar da zabe aka basu fom din.

“A ka’ida idan muka cike zamu kaiwa jam’iyya matakin karamar hukuma su sa hannu,daga nan mukai matakin jihar amma bisa mamaki bayan mun cike fom din saida muka yini muna neman wanda zai karba yasa hannu amma mun rasa.

 

“Jam’iyyar APC tayi taro ne kawai tare da sanar da son zuciyar su maimakon bari a fafata a zaben fidda gwani,” inji Sharada.

 

Siriki ne ya ya jagoranci zaben

Sha’aban Sharada ya ce jam’iyya ta turo mutum biyu a matsayin turawan zabe da daya daga cikin su sirikin Baffa Babba ne.

Ya kara da cewa shugabannin jam’iyya a karamar Hukumar birni da kudin tsarin jam’iyyar ya nemi su yi zabe su dari uku da tamanin ne.

Amma dari hudu da hudu ne suka kada kuri’a, da hakan ke nuna sun wuce adadin da kundin tsarin mulki ya tanada.

“wai mutum dari hudu sun zabe su mu kuma dan takarar mu ya samu kuri’a hudu.

“Lokacin da muka je filin zabe sai aka hana ainihin shugabanin jam’iyya katin makalawa da zai basu damar shiga suyi zabe,” inji shi.

Ya kara da cewa da anyi zabe kamar yadda kundun tsarin mulkin jam’iyya ya tanadar tabbas za su karbi kowanne irin sakamako.

“Kiri-kiri baturen zabe Yusuf Lajawa ya ce ba zaibi kundun tsarin mulkin jam’iyya ba, shi zayyi amfani da umarnin Abdullahi Abbas ne kawai.

Malam Sharada ya kuma ce suna shirye-shiryen daukar matakin da ya dace akan irin kama karyar da akayi masu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending