Connect with us

KANUN LABARAI

Bude iyakokin kasa : Minstar kudi, Minstan noma wa ke da gaskiya

Published

on

Al’umma a jihar Kano na ci gaba da bayyana ra’ayinsu kan baki biyu da aka samu na batun bude iyakokin kasar nan tsakanin ministan noma da ministar kudi.

Kano Focus ta rawaito cewa a ranar Talatar da ta gabatane dai ministar kudi, Zainab Shamsuna Ahmed  ta ce akwai yiwuwar a sake bude iyakokin kasar nan da aka rufe tun a watan Agustan bara.

Ministar ta bayyana hakanne a taron tattalin arzikin Najeriya da akayi a jihar Legas a ranar talatar makon jiya.

Ta ce kwamitin da shugaba Buhari ya kafa don duba ribar rufe iyakokin sun bashi shawarar budewa.

Sai dai kuma a ranar Asabar ne ministan aikin gona na kasa Muhammad Sabo Nanono ya bayyana cewa babu ranar da za a buɗe iyakokin kasar domin mukullin da aka garƙame iyakokin an cilla shi cikin teku.

Minista Sabo Nanono ya bayyana hakan ne a gurin bikin rabon kayan aikin gona ga manoman da ambaliyar ruwa ta rutsa da su a jihar Kebbi.

Ya ƙara da cewa har yanzu gwamnatin tarayya bata shirya buɗe iyakokin ƙasar nan ba, domin har yanzu tana nan akan bakarta na ganin harkar noma a ƙasar nan ta bunƙasa.

To ko me jama’ar gari ke cewa kan wadannan kalamai na minsitocin biyu?

Hajara Abdullahi Na’ibawa ta ce cin karo da juna da kalaman ministocin sukayi ya nuna karara yadda gwamnatin shugaba Buhari ta gaza ta fuskar jagoranci.

Ta ce wasa ne da hankalin al’ummar arewacin kasar nan kawai, shi yasa suke mi’ara koma baya a kalaman nasu.

“Arewa ba ta da masu tsaya mata kowa abinda ya shafe shi kawai yake yi manyan mu basu da wani amfani,” a cewar ta.

Abdullahi Yusuf Tukuntawa cewa ya yi babu magana daya a yadda gwamnati take tafiyar da al’amuranta.

Ya ce masalaha shi ne kawai a bude boda duba da halin da ‘yan kasa ke ciki na matsi da wahala, domin rufe ta da akayi bai canza komai ba sai ma kara ta azzara abubuwa da ya yi.

“Idan an rufe boda ne don ayi maganin matsalar tsaro to har yanzu matsalar kara ta’azzara ta ke yi, kalli abin takaici yadda aka kashe manoma da basu jiba basu gani ba a jihar Borno.

Shi kuwa Adamu Abdullahi cewa ya yi Allah ya jarabci kasarne da azzaluman shugabannin masu son zuciya.

Ya kara da cewa ba karamin abin kunya bane a ce ministoci a gwamnati guda daya amma suna magana dake karyata junan su.

“Tunda har boda tana rufe ba a samu tsaro ba to tabbas bude ta ma ba zai ta’azzara matsalar ba, sai dai ma ya magance ta domin komai zai sakko kuma ayyukan yi za su karu a kasar nan.

Ya kuma ce lokaci ya wuce da za a rinka yaudarar al’ummar arewacin kasar nan da batun bude boda don ba shi suke bukata ba face a magance musu matsalar tsaro.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Mutane 18,000 sun amfana da aikin ido kyauta ta Gidauniyar Mangal a Katsina

Published

on

 

Kimanin marasa lafiya masu rauni 18,000 da ke fama da cututtukan ido daban-daban a jihar Katsina sun amfana da ayyukan kulawar ido da tiyata kyauta da Gidauniyar Mangal ta dauki nauyi tun bayan kafuwarta a shekarar 2016.

 

Wani mamba na kwamitin amintattu (Board of Trustees) na gidauniyar, Malam Hussaini Kabir, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin kaddamar da aikin tiyatar ido na zangon karshe na shekarar 2025 a Cibiyar Ido ta Katsina.

 

Kabir ya bayyana cewa kimanin mutane 7,000 ne suka amfana a shekarar 2025 kadai, daga sassan jihar Katsina, jihohin makwabta, har ma da wasu yankuna na Jamhuriyar Nijar.

A cewarsa, gidauniyar ta fara tantance wadanda za su amfana kimanin makonni biyu da suka gabata, inda marasa lafiya da dama suka samu magunguna kyauta da tabarau na likita.

 

Kabir ya kara da cewa wadanda ke bukatar tiyata an dauki nauyin dukkan zaman asibitinsu gaba daya, yana mai cewa kimanin marasa lafiya 2,000 aka tantance a yayin aikin zangon karshe da ake ci gaba da yi.

Ya sake jaddada kudirin gidauniyar na inganta samun kulawar lafiya, yana bayyana shirin a matsayin wani bangare na nauyin alhakin zamantakewar kamfanoni (corporate social responsibility).

 

“Manufarmu ita ce tallafa wa kokarin gwamnati tare da rage nauyin kudin kula da lafiya ga mafi rauni, musamman wadanda ke fama da matsalar biyan bukatun rayuwa,” in ji shi.

Wani likitan ido a cibiyar, Dokta Ahmad Hamza, ya bayyana cewa an gano marasa lafiya da dama na fama da cutar idon toka (cataract) da glaucoma, cututtuka da galibi ke bukatar tiyata.

 

Ya jaddada muhimmancin duba ido akai-akai, yana mai cewa gano cuta da wuri na taimakawa wajen hana asarar gani ta dindindin da cututtukan ido masu zuwa a boye ke haifarwa, kamar glaucoma, cataract da lalacewar macula (macular degeneration).

Daya daga cikin wadanda suka amfana, Malam Yusufa Usman, ya ce ya shafe sama da shekaru biyu yana fama da matsalar gani amma ba shi da ikon biyan kudin tiyata.

 

“Tsawon shekaru biyu ban iya gani sosai ba, amma yau na yi tiyata kuma ina da fatan ganina zai dawo.

Ina rokon Allah Madaukakin Sarki ya saka wa Gidauniyar Mangal da alheri bisa wannan kyakkyawan aiki.

 

“Ina fatan sauran masu kudi za su yi koyi da wannan abin a yaba,” in ji Usman.

Wata mai amfana, Aisha Muntari daga kauyen Bakuru, ta bayyana kwarewarta yayin da take jiran a kai ta dakin tiyata.

 

Muntari ta ce ta kamu da matsalar ido kimanin shekara guda da ta wuce kuma ta kusa yanke tsammani kafin ta samu labarin shigar gidauniyar, tana mai bayyana kwarin gwiwar cewa nan ba da dadewa ba ganinta zai dawo.

Continue Reading

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Trending