Connect with us

Hausa

Dalilai 4 da ya hana Teloli samun dinki a bana

Published

on

Zulaiha Danjma

Teloli a jihar Kano sun koka kan karancin dinkin sallah da jama’a ke kawo musu, biyo bayan matsin rayuwa da ake ciki.

Kano Focus ta rawaito cewa Telolin sun bayanna dalilai hudu da ke kara ta’azzara rashin samun aikin.

Cikin kuwa har da karin kudin kayan dinki, Rashin kudi a hannun jama’a, dawurwuran tsayar da zabi, da kuma rashin samun albashi.

Karin kudin kayan dinki

A cewar wani tela Abdussalam Kabir da ke dinki a unugwar Rijiyar Zaki, kudaden da tela yake siyan kayan dinki sun yi tashin gwauron zabo.

“A gaskiya komai ya canza, saboda tsadar kayan dinkin, samun dinki ya ragu”

“Wasu abubuwan da ake siya  ada N600 yanzu ya koma N800

“Me dinka set 4 ada da wuya yanzu ya dinka kala daya” Acewarsa.

Shi ma wani tela Kabiru Abubakar da ke Tudun Maliki  ya ce kudaden siyan kayan aiki a bana sun nunka.

“Kudin siyan kayayyakin dinki sun karu gaskiya, wasu sun ninka kudinsu akan yadda aka sansu”

“Kananan kamar zare wani dan N40 ya dawo N50, kuma quality na kayan ma duk  sun ragu.

“Shi komai da komai yadda aka sanshi ya ragu a quality ga kuma kudin sa ya karu” Acewar sa.

Rashin kudi 

Telolin sun cigaba da cewa rashin kudi na hana abokan huldarsu  kawo dinki.

Kabiru Muhammad ya ce, masu kawo dinki sun sauya daga yadda suka saba kawowa ba kamar a baya ba.

“Idan kostoma ada na kawo kaya kala 3, yanzunma zai iya kawo ukun amma za kaga darajar kanyan sun ragu.

“Alalmisali ace  bara sun kawo maka shadda me tsada wanda duk yadi zai iya kaiwa 2,500 zuwa 3,000 yanzu sai an rage kudin.

“sai ka gama mutum yaje ya siyo yadi, irin su Lana ko Kashmir ko irin su dan Aba dan ya samu rarar kudi.

“Wannan ragowar canjin da aka samu zai iya biyan kudin dikin dasu”

Haka zalika, Abdulsalam Muhammad ya ce “yara ma da iyayensu ke dinka musu kala 4 ko 3 yanzu da wuya a yi musu kala 2 saboda ba kudin”

“Kusan dai duk wanda ya kawo dinkin yaransa ba sama da guda biyu-biyu” Acewar sa

Rashin takamai-mai

Haka zalika Telolin sun bayyana cewa mafi akasari magidanta na shiga halin dawurwura da rashin takamai-mai wajen zabin mai za su dinka da iyalansu.

Wasu na tuna ni biyu, tsakanin dinkin da wasu al’amuran na gida wanne ne ya fi amfami.

“Mafi akasari ta abinci ake bata sutura ba, wani gani yake mai zai yi, shin dinkin ya kamata ya yi, ko abincin yara yakamata ya siya, ko kudin makarantar yara zai biya.

“Irin wannan matsololin da suke faruwa shi ne yake sa muke fuskanta karancin kawo dinki”

“Amma duk da hakan mutane na yin iya bakin kokarinsu wajen ganin sun yi ma kansu da iyalen su sutura” Acewarsa, a cewar Kabiru tela.

Rashin Albashi 

Telolin sun bayyana cewa  rashin biyan albashi na sanya jama’a kasa kai musu dinky, tunda galibin al’umma yan albashi ne.

“Gaskiya wannan lokacin ana samun karancin samun kayan dinki musamman ma wasu ba a biya albashi ba.

“Wani yana jiran sai an biya, inda zai iya kasancewa sai karshe-karshen azumi za a biya, kuma lokacin wani ma zai tunanin dinkin”

Shi ma Kabiru tela yace “Wasu rashin albashi ne da wuri, wani za kaga gwamnatin ta ba da albashin amma ta cire wani baa’ari daga ciki.

“Wani lokacin ma ba a biya albashin akan lokaci ba ko dai wasu abubuwa makaman cin haka” Acwarsa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

FG kickstarts construction of Emerging Technologies Institute in Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

As part of significant milestone in the Federal Government of Nigeria’s efforts to secure the socio-economic wellbeing of the future generation, as the ground was opened for commencement of construction of the Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI) under the aegis of the National Agency for Science and Engineering Infrastructure (NASENI), The Presidency.

 

KKANO FOCUS reports that the Executive Vice Chaiman/Chief Executive Officer (EVC/CEO) of NASENI, Mr. Khalil Suleiman Halilu during the Ground-breaking ceremony held at the Bayero University Kano (BUK) New Campus said the new institute sits on 30 hectares of the BUK land to be built, featuring state-of-the-art facilities, including innovation hubs devoted to Artificial Intelligence and other cutting-edge technologies, complemented by reliable power supply. “NASENI will fully build and equip and support the new Institute” said the EVC/CEO.

 

The future of socio-economic development for nations rests on human creativity, innovation and cooperation, Artificial intelligence, robotics amongst others.

 

Halilu said that the establishment of SETI in Nigeria is to rapidly respond to the waves of young people globally revolutionizing world economies with unprecedented emergence of socio-economic frontiers as by-products of innovations and ingenuities of these young minds.

 

“We in NASENI are firm believers in the potential of young Nigerians to be the prime catalysts of the type of transformation that Nigeria requires. And we will do everything within our powers to support them to fulfil this important responsibility”

 

“We are gathered here today to kickstart a project that will transform the lives and careers of future generations of young Nigerians. The Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI), located at the Bayero University Kano (BUK) by NASENI. This is very much in line with our operating principles; what we call our 3Cs: Collaboration, Creation, and Commercialization. These 3Cs are the principles that passionately drive us and guide the work that we do to ensure the industrialization of Nigeria in line with the Renewed Hope agenda of President Bola Ahmed Tinubu.”

 

SETI will produce innovators, technologists, entrepreneurs who will make their mark not just in Nigeria but around the world. “I’m eagerly looking forward to the day, not too long from now, when the Institute’s first set of beneficiaries will astonish the world with what they’re capable of accomplishing. These stories will put not just BUK on the global innovation map, but also Kano State and the entire Nigeria” said Halilu.

 

While carrying out the symbolic foundation laying ceremony of the institute as Special Guest of Honour, the Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, described the project as not only laudable but NASENI’s another way of fast-tracking  the placing of Nigeria on the global map of innovation and industrialization. The minister called the project an “ace project” and a pointer to secure a veritable socio-economic development for the nation.

 

In his goodwill message, the Vice Chancellor of BUK, Professor Sagir Adamu Abbas described the new institute as a vehicle for bringing together the three critical tripods for economic and sustainable development for nations, that is, the government, academia and industry. He described the ground-breaking event as the beginning of Nigeria’s journey in pursuit of sustainable development, massive job creation opportunities for the youths, and that the BUK was delighted to be host to such laudable initiative and momentum.

 

There is also, in addition to SETI, a second NASENI project for BUK is an Agri-preneurship Training Hub, that will be equipped with modern greenhouses, and facilities for Soil-less Farming, and Tissue Culture; occupying 10 hectares of land at the Old Campus. These projects collectively represent what NASENI stands for, that is, building capacity, advancing industrialization, supporting economic growth and prosperity.

 

NASENI appreciates the Government and people of Kano State, and the Vice Chancellor, management and students of Bayero University Kano (BUK), for all the support. Special gratitude goes to the Honourable Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, the Special Guest of Honour.

 

NASENI thanked members of the National Assembly for their support, especially the NASENI oversight Committees in both chambers. And of course, President Bola Ahmed Tinubu, who has given NASENI the opportunity to serve Nigeria through his unwavering demonstration of commitment to the success of the Agency.

Continue Reading

Hausa

Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Published

on

Jaafar Jaafar

 

Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.

 

Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

 

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.

 

Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!

 

Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.

 

Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.

 

Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.

 

Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.

 

Allah Ya zaunar da mu lafiya.

Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook. 

 

Continue Reading

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Trending