LABARAI
Rundunar ‘yan sanda ta musanta kashe matashi a Kano
Aminu Abdullahi
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta musanta zargin da ake mata na kisan wani matashi mai suna Saifullahi Sani a unguwar Kofar Mata dake birnin Kano.
Kano Focus ta ruwaito cewar wannan na kunshe ne cikim wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar a ranar litinin.
Sanarwar ta ruwaito kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano Habu A Sani na cewa hukumar ta samu sanarwa cewa ‘yan daba na fada a unguwar Kofar Mata a jiya Lahadi.
A cewar sa hakan ce ta sanya runudunar ta tura jami’anta domin dai-daita al’amura.
Yace yayin kai daukin ne hukumar ta samu nasarar kama mutum biyu da ake zargi, rike da wukake.
Ya ce Hukumar ta kama matshi ne bayan da tuni aka soke shi da wuka a jikinsa tare da wani jami’in dan sanda.
Bayan da aka kai shi asibiti ne kuma ya mutu a can, inda shi kuma dan sandan aka mai da shi wani asibitin domin ci gaba da karbar magani.
Idan ba a manta ba a yau litinin ne al’ummar yankin Kofar Mata suka fito zanga -zanga dan nuna fushin su kan zargin da suke yiwa jami’an ‘yan sanda na kashe wani matashi Saifullahi Sani Musa mai shekaru 23.
matasa da dama ne suka mamaye titin Kofar mata da kewaye suna kona tayoyi tare da hana jama’a wucewa domin nuna adawar su da kisan matashin.
mahaifin matashin Sani Musa Kofar Mata ya shaidawa Kano Focus cewa da misalin karfe daya na dare jami’an yan sanda suka kai sumame unguwar suka kuma kama dan nasa lokacin da yake bacci a kofar gida.
Mista Musa ya kara da cewa bayan da gari ya waye yana kokarin tafiya ofishin yan sandan ne guda daga cikin yan kwamitin unguwar ya shaida masa cewar yan sanda sun kashe dan nasa.
Ya kara da cewa dan kwamitin ne ya shaida masa gawar dan nasa tana sashen bada agajin gaggawa na asibitin murtala amma za su kaita dakin ajiyar gawawwaki.
Malam Musa yace akwai raunukan duka da dama a jikin yaron da yake zargin jami’an ‘yan sanda sunyi masa.
Shima wanda ke tare da mamacin a lokacin da jami’an ‘yan sandan suka zo samamen Hamisu Muhammad yace suna bacci yayin da ‘yan sandan suka zo.
ya kara da cewa daga nan ne suka yi yinkurin tafiya dasu wanda shi kuma yasamu nasarar tsarewa.
To sai dai rundunar yan sadan ta musanta wannan zargi inda ta ce kokadan bata da hannu kan kisan matashin.
Hausa
Mutane 18,000 sun amfana da aikin ido kyauta ta Gidauniyar Mangal a Katsina
Kimanin marasa lafiya masu rauni 18,000 da ke fama da cututtukan ido daban-daban a jihar Katsina sun amfana da ayyukan kulawar ido da tiyata kyauta da Gidauniyar Mangal ta dauki nauyi tun bayan kafuwarta a shekarar 2016.
Wani mamba na kwamitin amintattu (Board of Trustees) na gidauniyar, Malam Hussaini Kabir, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin kaddamar da aikin tiyatar ido na zangon karshe na shekarar 2025 a Cibiyar Ido ta Katsina.
Kabir ya bayyana cewa kimanin mutane 7,000 ne suka amfana a shekarar 2025 kadai, daga sassan jihar Katsina, jihohin makwabta, har ma da wasu yankuna na Jamhuriyar Nijar.

A cewarsa, gidauniyar ta fara tantance wadanda za su amfana kimanin makonni biyu da suka gabata, inda marasa lafiya da dama suka samu magunguna kyauta da tabarau na likita.
Kabir ya kara da cewa wadanda ke bukatar tiyata an dauki nauyin dukkan zaman asibitinsu gaba daya, yana mai cewa kimanin marasa lafiya 2,000 aka tantance a yayin aikin zangon karshe da ake ci gaba da yi.

Ya sake jaddada kudirin gidauniyar na inganta samun kulawar lafiya, yana bayyana shirin a matsayin wani bangare na nauyin alhakin zamantakewar kamfanoni (corporate social responsibility).
“Manufarmu ita ce tallafa wa kokarin gwamnati tare da rage nauyin kudin kula da lafiya ga mafi rauni, musamman wadanda ke fama da matsalar biyan bukatun rayuwa,” in ji shi.

Wani likitan ido a cibiyar, Dokta Ahmad Hamza, ya bayyana cewa an gano marasa lafiya da dama na fama da cutar idon toka (cataract) da glaucoma, cututtuka da galibi ke bukatar tiyata.
Ya jaddada muhimmancin duba ido akai-akai, yana mai cewa gano cuta da wuri na taimakawa wajen hana asarar gani ta dindindin da cututtukan ido masu zuwa a boye ke haifarwa, kamar glaucoma, cataract da lalacewar macula (macular degeneration).

Daya daga cikin wadanda suka amfana, Malam Yusufa Usman, ya ce ya shafe sama da shekaru biyu yana fama da matsalar gani amma ba shi da ikon biyan kudin tiyata.
“Tsawon shekaru biyu ban iya gani sosai ba, amma yau na yi tiyata kuma ina da fatan ganina zai dawo.
Ina rokon Allah Madaukakin Sarki ya saka wa Gidauniyar Mangal da alheri bisa wannan kyakkyawan aiki.
“Ina fatan sauran masu kudi za su yi koyi da wannan abin a yaba,” in ji Usman.

Wata mai amfana, Aisha Muntari daga kauyen Bakuru, ta bayyana kwarewarta yayin da take jiran a kai ta dakin tiyata.
Muntari ta ce ta kamu da matsalar ido kimanin shekara guda da ta wuce kuma ta kusa yanke tsammani kafin ta samu labarin shigar gidauniyar, tana mai bayyana kwarin gwiwar cewa nan ba da dadewa ba ganinta zai dawo.
Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano
Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”
Headlines
Kano State Reforms: Sa’adatu Rimi University Reverts to College of Education Status
The Kano State Executive Council has approved the conversion of Sa’adatu Rimi University of Education back to Sa’adatu Rimi College of Education, Kumbotso, while maintaining its status as a degree-awarding institution.
In a statement issued by the Commissioner for Information and Internal Affairs, Baba Halilu Dantiye, the decision was made to enhance educational quality and streamline management in the state’s higher education sector.
The move follows the 18th meeting of the Executive Council, held on September 18, 2024, after extensive consultations with stakeholders and recommendations from a high-powered committee tasked with reviewing the institution’s status.
The committee raised concerns over the transition to university status, citing risks such as the potential loss of experienced lecturers, salary disputes, and administrative challenges.
Dantiye noted that similar institutions nationwide have operated successfully as colleges of education while offering degree programs through the “Dual Mode” system, as introduced by the National Commission for Colleges of Education (NCE).
This system allows institutions to maintain their core structure while expanding their academic offerings.
Governor Abba Kabir Yusuf has approved the immediate dissolution of the university’s management, with the Vice Chancellor directed to hand over to his most senior deputy.
The government assured that current students would not be affected, as they will continue their studies without disruption.
Additionally, the university’s certificate will be preserved for future use, and the institution will continue to offer both its traditional courses and new degree programs.
This strategic decision underscores the Kano State Government’s commitment to ensuring the growth, stability, and academic excellence of its educational institutions.
