Connect with us

LABARAI

Zanga-zanga ta barke bayan da aka zargi jami’an ‘yan sanda da kisan matashi a Kano

Published

on

Aminu Abdullah

Al umma da dama ne suka  fito zanga zanga a unguwar kofar mata dake cikin birnin Kano dan nuna fushin su kan zargin da suke yiwa jami’an ‘yan sanda na kashe wani matashi  Saifullahi Sani Musa mai shekaru 23.

Kano Focus ta ruwaito cewa matasa da dama ne suka mamaye titin Kofar mata da ke waye a da safiyar yau litinin, suna kona tayoyi tare da hana jama’a wucewa domin nuna adawar su da kisan matashin.

mahaifin matashin Sani Musa Kofar Mata ya shaidawa Kano Focus cewa da misalin karfe daya na dare jami’an yan sanda suka kai sumame unguwar suka kuma kama dan nasa lokacin da yake bacci a kafar gida.

“Yaro na kowa ya sanshi baya shan komai hasalima akwance yake a kofar gida saboda zafi.

“Bayan sun kamashi a daren naje ofishin ‘yan sanda sai akacemin ai tunda yan sanda ne na bari da safe naje,” a cewar mahaifin yaron.

Mista Musa ya kara da cewa bayan da gari ya waye yana kokarin tafiya ofishin yan sandan ne guda daga cikin yan kwamitin unguwar ya shaida masa cewar yan sanda sun kashe dan nasa.

Ya kara da cewa dan kwamitin ne ya shaida masa gawar dan nasa tana sashen bada agajin gaggawa na asibitin murtala amma zasu kaita dakin ajiyar gawawwaki

Malam Musa yace akwai raunukan duka da dama a jikin yaron da yake zargin jami’an ‘yan sanda sunyi masa.

Shima wanda ke tare da mamacin a lokacin da jami’an ‘yan sandan suka zo samamen Hamisu Muhammad yace suna bacci yayin da ‘yan sandan suka zo.

ya kara da cewa daga nan ne suka yi yinkurin tafiya dasu wanda shi kuma yasamu nasarar tsarewa.

“Baya shaye-shaye ko hayakin taba ma baya son shaka kuma basu kamashi da komai ba amma suka kasheshi wannan zalinci dayawa yake,” in ji Malam Hamisu.

Daya daga cikin yan uwan mamacin Musa Dahiru Kofar Mata cewa ya yi ‘yan sandan sun shigo cikin unguwar ne da daddare Inda suka rinka harba bindiga wanda daga bisani sukayi awan gaba da yaron da yake bacci da sauran yara.

Ya kuma ce bayan duka da suka lakadawa mamacin haka zalika sun sare shi a jiki.

Mista Dahiru yace suna bukatar hukuma ta dauki mataki akan kisan da akayiwa yaron tare da hukunta duk wanda keda hannu a cikin al’amarin.

A nasa bangaren mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Kano Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce sun samu labarin afkuwar lamarin kuma suna cigaba da gudanar da bincike.

 

 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Headlines

Kano State Reforms: Sa’adatu Rimi University Reverts to College of Education Status

Published

on

The Kano State Executive Council has approved the conversion of Sa’adatu Rimi University of Education back to Sa’adatu Rimi College of Education, Kumbotso, while maintaining its status as a degree-awarding institution.

In a statement issued by the Commissioner for Information and Internal Affairs, Baba Halilu Dantiye, the decision was made to enhance educational quality and streamline management in the state’s higher education sector.

The move follows the 18th meeting of the Executive Council, held on September 18, 2024, after extensive consultations with stakeholders and recommendations from a high-powered committee tasked with reviewing the institution’s status.

The committee raised concerns over the transition to university status, citing risks such as the potential loss of experienced lecturers, salary disputes, and administrative challenges.

Dantiye noted that similar institutions nationwide have operated successfully as colleges of education while offering degree programs through the “Dual Mode” system, as introduced by the National Commission for Colleges of Education (NCE).

This system allows institutions to maintain their core structure while expanding their academic offerings.

Governor Abba Kabir Yusuf has approved the immediate dissolution of the university’s management, with the Vice Chancellor directed to hand over to his most senior deputy.

The government assured that current students would not be affected, as they will continue their studies without disruption.

Additionally, the university’s certificate will be preserved for future use, and the institution will continue to offer both its traditional courses and new degree programs.

This strategic decision underscores the Kano State Government’s commitment to ensuring the growth, stability, and academic excellence of its educational institutions.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending