KANUN LABARAI
Zanga-zanga: yadda aka kashe yarana hudu a Kano.
Mukhtar Yahya Usman
Hajiya Hadiza Shareef da ke unguwar rijiyar lemo a nan Kano ta ce yaranta hudu da ke yi mata aikatau aka kashe ya yin zanga-zangar @EndSARS a Kano.
A wata hira ta musamman da jaridar Kano Focus a ranar juma’a ta ce yaran nata na kular mata da gidan ‘Wanka da Bahaya’ da ke Middle Road a unuwar Sabon Gari.
Ta bayyana matasan da aka kashe da Abdurrahman Sobo wanda ya fito daga garin Minjibir kuma yake aikatau a hannunta tsahon shekaru biyu.
Sai Kuma Jamilu Muhammad da ke unguwar Zoo rood a nan birinin Kano da shi ma ya shafe sama da shekara yana yi mata aikatau,

Sai kuma na uku Aliyu Shehu da ake yiwa lakabi da Gatari mutumin sheka makaranta a nan birnin Kano.
Cikon na hudun shi ne Badamasi Ibrahim da ya zo ci rani daga Katsina, yake kuma zaune a unguwar Jaba.
Hajiya Hadiza ta ce mutum uku daga cikin wadannan an samu gawar su biyu ma har an yi musu jana’iza ya yin da daya har yanzu yake mutuware a asibitin Murtala.
Sai dai ta ce cikon na hudu wato Abdurraman Sobo an koneshi kurmus ne ba su iya tantance gawar sa ba kamar na ragowar.
Yadda al’marin ya faru
A cewar Hajiya Hadiza an mamayi yaran nata ne cikin dare a ranar Talata da ta gabata inda wasu matasa dauke da makamai da galibinsu inyamuraine suka kewaye gidan da yaran nata ke yi mata aikatau da nifin Hallaka su.
“A ranar Talatar da ta gabata ‘Da’ na Arabi ya kirani a waya ya ce naje na debo yarana wato kannensa daga makaranta ana tashin hankali.
“Ba shiri na tafi na debo su, da yake suna karatu ne a makarantar Tony Chetta.
“Sai na ce mishi suma su rufe wurin nasu da suke sana’ar su taho gida, sai ya ce ba komai an kwantar da tarzomar.
Da magariba na sake kiransu na ce ku fito daga wurin nan kungani ya zama kamar fadan kabilanci da Inyamuran kunce suna ta dukan Hausawa, sai ya ce min ba komai, wuta ta lafa.” A cewar ta.
Cikin dare aka kai musu hari
Hajiya Hadiza ta kara da cewa bayan wannan tattaunawa da yaron nata ne kuma ta kara samun waya marar dadi cikin dare.
“Karfe 3:00 na dare sai Arabi ya sake kirana ya ce gabadaya Inyamuran nan sun sake yi musu kawanya.
“da yake yaran namu a ciki suke kwana kuma wannan gidan shi kadai na Hausawa a yankin, don haka suka mayar da hankali a kansa.
“Bayan da aka yi hatsaniyar da rana kura ta lafa shi ne fa suka sake komawa cikin dare suka yi musu kawanya suka kashe na kashewa suka kona na Konawa”. A cewar ta.
Da kyar muka sha da ranmu
Arabi Sahrif Hadi da ke zaman Da ga hajiya Hadiza da kuma ke kula da gidan wankan ya shaidawa Kano Focus yadda suka tsira da ransu kuma sauran abokan sana’ar sa suka salwanta.
Ya ce bayan kura ta lafa a zanga-zngar ranar Talata bayan magriba sai wasu gungun matasa da makamai suka taso musu kamar za su hallakasu.
“Sun yo kan mu da makamai muka ce musu mu ina ruwan mu ba fada muke da sub a, muka dai samu muka gudu muka shiga muka kulle.
“Sunyi ta kokarin balla gidan amma Allah bai basu sa a ba sai suka hakura suka koma.
“munan zaune cikin razani da firgici domin kowa ya kasa tafiya gida a nan muka kwana, da misalin karfe uku saura muka fara jiyo ihu da hayaniya sai wuta ke tashi ta ko ina.
“”suka zo suna dukan gidan suna mu bude idan ba haka ba za su hauro sai sun kashe kowa, suka bankara Kofar cikin ikon Allah basu samu sun karya ba.
“to bayan munji kamar sunja bayan ne wasu daga cikin mu sai suka fita suka ruga don menan ceton ransu ni kuma na tsallaka wani Hotel da ke kusa da mua na fake.
“shi Badamsi ya na fita suka bigeshi sai gawar sa muka gani da safe a cikin kwata, shi kuma Abdurrahman Sobo ga shinan kusa da Badamasi an saka masata taya an kone shi kurmus ko da dai bamu ganeshi ba amma dai ina kyautata zaton shi ne.
“Sauran yara kuma akwai sabbin gine-gine da aka yi da ba a kammala ba sai suka bude sokaway din suka shiga suka buya, wasu kuma suka buya cikin ciyayi, wannan shi ne abin da ya faru cikin dare.”
Arabi ya shaidawa Kano Focus cewar duk da wannan al’amari da ya faru cikin dare washe gari suka sake dawowa suka nemi balla gidan domin su cimmusu.
“bayan sun dawo washe gari ne suka kuma koramu muka shiga muka kulle yara suka ruga aguje neman mafita.
“Muna gani akan idon mu aka dauki Jamilu aka dannashi a cikin duron da suka kunnawa wuta ya kuma kone kurmus akan idon mu.
“Akwai wani Abuakar shima muna gani suka dannashi a cikin doron ya kone kurmus. A cewar sa.
Ya kuma ce kafatanin wadanda suka mutu an aike da gawarwakin su dakin adana gawarwaki na asibitin Murtala da ke nan Kano.
Haka zalika tuni wasu da ga cikin su ‘yan uwansu suka fara karbar gawawwakin su domin yi musu suttura.

Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

Hausa
Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Nasiru Yusuf Ibrahim
Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.
Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.
Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.
A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.
Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Hausa
Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Nasiru Yusuf Ibrahim
Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.
Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.
Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.
A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.
