Connect with us

KANUN LABARAI

Zanga-zanga: yadda aka kashe yarana hudu a Kano.

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

Hajiya Hadiza Shareef da ke unguwar rijiyar lemo a nan Kano  ta ce yaranta hudu da ke yi mata aikatau aka kashe ya yin zanga-zangar @EndSARS a Kano.

A wata hira ta musamman da jaridar Kano Focus a ranar juma’a ta ce yaran nata na kular mata da gidan ‘Wanka da Bahaya’ da ke Middle Road a unuwar Sabon Gari.

Ta bayyana matasan da aka kashe da Abdurrahman Sobo wanda ya fito daga garin Minjibir kuma yake aikatau a hannunta tsahon shekaru biyu.

Sai Kuma Jamilu Muhammad da ke unguwar Zoo rood a nan birinin Kano da shi ma ya shafe sama da shekara yana yi mata aikatau,

Sai kuma na uku Aliyu Shehu da ake yiwa lakabi da Gatari mutumin sheka makaranta a nan birnin Kano.

Cikon na hudun shi ne Badamasi Ibrahim da ya zo ci rani daga Katsina, yake kuma zaune a unguwar Jaba.

Hajiya Hadiza ta ce mutum uku daga cikin wadannan an samu gawar su biyu ma har an yi musu jana’iza ya yin da daya har yanzu yake mutuware a asibitin Murtala.

Sai dai ta ce cikon na hudu wato Abdurraman Sobo an koneshi kurmus ne ba su iya tantance gawar sa ba kamar na ragowar.

Yadda al’marin ya faru

A cewar Hajiya Hadiza an mamayi yaran nata ne cikin dare  a ranar Talata da ta gabata inda wasu matasa dauke da makamai da galibinsu inyamuraine suka kewaye gidan da yaran nata ke yi mata aikatau da nifin Hallaka su.

“A ranar Talatar da ta gabata ‘Da’ na Arabi ya kirani a waya ya ce naje na debo yarana wato kannensa daga makaranta ana tashin hankali.

“Ba shiri na tafi na debo su, da yake suna karatu ne a makarantar Tony Chetta.

“Sai na ce mishi suma su rufe wurin nasu da suke sana’ar su taho gida, sai ya ce ba komai an kwantar da tarzomar.

Da magariba na sake kiransu na ce ku fito daga wurin nan kungani ya zama kamar fadan kabilanci da Inyamuran kunce suna ta dukan Hausawa, sai ya ce min ba komai, wuta ta lafa.” A cewar ta.

Cikin dare aka kai musu hari

Hajiya Hadiza ta kara da cewa bayan wannan tattaunawa da yaron nata ne kuma ta kara samun waya marar dadi cikin dare.

“Karfe 3:00 na dare sai Arabi ya sake kirana ya ce gabadaya Inyamuran nan sun sake yi musu kawanya.

“da yake yaran namu a ciki suke kwana kuma wannan gidan shi kadai na Hausawa a yankin, don haka suka mayar da hankali a kansa.

“Bayan da aka yi hatsaniyar da rana kura ta lafa shi ne fa suka sake komawa cikin dare suka yi musu kawanya suka kashe na kashewa suka kona na Konawa”. A cewar ta.

Da kyar muka sha da ranmu

Arabi Sahrif Hadi da ke zaman Da ga hajiya Hadiza da kuma ke kula da gidan wankan ya shaidawa Kano Focus yadda suka tsira da ransu kuma sauran abokan sana’ar sa suka salwanta.

Ya ce bayan kura ta lafa a zanga-zngar ranar Talata bayan magriba sai wasu gungun matasa da makamai suka taso musu kamar za su hallakasu.

“Sun yo kan mu da makamai muka ce musu mu ina ruwan mu ba fada muke da sub a, muka dai samu muka gudu muka shiga muka kulle.

“Sunyi ta kokarin balla gidan amma Allah bai basu sa a ba sai suka hakura suka koma.

“munan zaune cikin razani da firgici domin kowa ya kasa tafiya gida a nan muka kwana, da misalin karfe uku saura muka fara jiyo ihu da hayaniya sai wuta ke tashi ta ko ina.

“”suka zo suna dukan gidan suna mu bude idan ba haka ba za su hauro sai sun kashe kowa, suka bankara Kofar cikin ikon Allah basu samu sun karya ba.

“to bayan munji kamar sunja bayan ne wasu daga cikin mu sai suka fita suka ruga don menan ceton ransu ni kuma na tsallaka wani Hotel da ke kusa da mua na fake.

“shi Badamsi ya na fita suka bigeshi sai gawar sa muka gani da safe a cikin kwata, shi kuma Abdurrahman Sobo ga shinan kusa da Badamasi an saka masata taya an kone shi kurmus ko da dai bamu ganeshi ba amma dai ina kyautata zaton shi ne.

“Sauran yara kuma akwai sabbin gine-gine da aka yi da ba a kammala ba sai suka bude sokaway din suka shiga suka buya, wasu kuma suka buya cikin ciyayi, wannan shi ne abin da ya faru cikin dare.”

Arabi ya shaidawa Kano Focus cewar duk da wannan al’amari da ya faru cikin dare washe gari suka sake dawowa suka nemi balla gidan domin su cimmusu.

“bayan sun dawo washe gari ne suka kuma koramu muka shiga muka kulle yara suka ruga aguje neman mafita.

“Muna gani akan idon mu aka dauki Jamilu aka dannashi a cikin duron da suka kunnawa wuta ya kuma kone kurmus akan idon mu.

“Akwai wani Abuakar shima muna gani suka dannashi a cikin doron ya kone kurmus. A cewar sa.

Ya kuma ce kafatanin wadanda suka mutu an aike da gawarwakin su dakin adana gawarwaki na asibitin Murtala da ke nan Kano.

Haka zalika tuni wasu da ga cikin su ‘yan uwansu suka fara karbar gawawwakin su domin yi musu suttura.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending