Connect with us

KANUN LABARAI

Rashin baiwa kananan hukumomi kudadensu ne ke kawo talauci a kasar nan-Bappa Yola

Published

on

Nasiru Yusuf

Mai taimakawa shugaban kasa na musamman kan harkokin siyasa Malam Abdurrahman Bappa Yola ya ce rikewa Kananan hukumomi kason da gwamnatin tarayya ke ba su ne ke ruruta wutar talauci a Najeriya.

Kano Focus ta ruwaito Abdurrahman Bappa Yola ya bayyana hakan ne lokacin taron kaddamar da gamayyar wasu kungiyoyi biyar da suka hadu karkashin sabuwar laima da suka kira ‘CoDEN’.

Malam Yola ya ce baya ga talauci, rashin ba wa ‘Kananan Hukumomi’ kudadensu ya haifar da matsalolin tsaro dake samun kasar nan.

“Rashin samun kudin Kananan Hukumomi shi ne ya kai mu yau, wato talauci da yai yawa a Kananan Hukumomi wanda ya haifar da matsaloli da dama musamman harka ta tsaro.

“Wannan rashin ba wa Kananan Hukumomi kudadensu ya jawo matsala ta talauci wadda ta haifar mana da rashin tsaro.

“Wannan yana da muhimmamnci kwarai da gaske, ya zama cewa Kananan Hukumomi suna cin gashin kan su.

“Manufa gwamnoni su dai na tare kudadensu a Jiha, su ba su kudinsu ya tafi kasa ai musu aiki da shi,” a cewar Malam AbdurRahman Yola.

Ya cigaba da cewa kamata ya yi idan gwamnatin tarayya ta turowa Kananan Hukumomi kasonsu na wata-wata, to lallai ne ya je musu.

Mai taimakawa shugaban Kasar ya ce hakan shi ne zai magance zargin da ake yi wa gwamnatocin jihohi da na tarayya na gazawarsu kan yadda abubuwa ba sa tafiya dai-dai.

Malam Abdurrahman Bappa Yola ya bugi kirjin cewa, tun da gwamnatin shugaba Muhammad Buhari ta hau mulki ba wata Jiha da aka rike mata kasonta daga gwamnatin tarayya, don haka bai ga dalilin da jihohi za su cigaba da rikewa kananan Hukumomi kasonsu ba.

Ya ce irin wannan gwamnatin tarayya take so Jihohi su yi wa Kananan Hukumomi don arziki ya yalwata.

Game da me gwamnatin tarayya ke yi na tabbatar da gwamnoni sun bi umarnin da ta bayar na bai wa Kananan Hukumomi kudadensu, Bappa Yola ya ce

“Gwamnatin Tarayya ta yi na ta, a tsari, duk inda Dimokuradiyya take, Kungiyoyi irin CoDEN ne yakamata su dau gabarar tabbatar da gwamnatocin jihohi sun tabbatar wannan tsari ya tabbatar. Shi ya sa ni ma na zo wannan taro.” Ya ce.

A jawabin sa Farfesa Kamilu Fagge na jami’ar Bayero da ke nan Kano  ya ce irin wadannan tarurruka kan taimakawa mulkin Dimokuradiyya.

A cewar sa ta hakan za a san mai yake damun mutane, kuma ya za a yi a warware  matsalar don cigaban al’umma.

Daya daga cikin wadanda suka samar da gamayyar ta ‘CoDEN’ Malam Abdullahi Sule daga Kungiyar YEDA ya ce manufar gamayyar shi ne samar da ingantacciyyar Dimokuradiyya da za ta amfani kowa da kowa.

Ya ce manufar su shi ne, tabbatar da cewar kudaden Kananan Hukumomi da na Majalisar Jihohi suna isa asusunsu kai tsaye kuma suna kashe kudadensu ba tare da katsalandan din gwamnoni ba.

Malam Abdullahi Sule ya ce Kungiyoyin da suka samar da gamayyar ta ‘CoDEN’ su ne YEDA da CAJA da CDE da OCCEN da Kuma Renaissance Coalition.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending