Connect with us

KANUN LABARAI

Makafi da guragu za su tsaya takarar chairman da kansila a Kano

Published

on

Aminu Abdullah

Masu bukata ta musamman da suka hadar da guragu da makafi  ne suka bayyana aniyarsu ta tsayawa takarar chairman da kansila a zaben kananan hukumomi da ke tafe.

Kano Focus ta ruwaito cewa duk da irin kalubalen da suke fuskanta na rayuwa amma sunce bana suma sai an dama da su.

A tattaunawar jaridar Kano Focus da shugaban kungiyar masu bukata ta musamman a nan Kano malam Musa Muhammad Shaga, ya ce akwai nau’ikan masu bukata ta musaman da za su shiga zabe a fafata da su.

Malam Shaga ya ce Jamilu Ali Haruna da ke takarar shugabancin karamar hukumar Bunkure makahone da kuma tuni ya siyi takardar tsayawa takara.

Haka kuma akwai Adamu Ibrahim Maikoriya da yake ta karar Kansila a unguwar Sani Mainagge dake karamar hukumar Gwale da shima makaho ne.

Yace dukkan ‘yan takarar sun riga sun sayi takardar tsayawa takara kamar yadda doka ta tanada, kawai suna jiran a shiga zabe ne.

A cewar sa rabon da a samu wani mai bukata ta musamman ya shiga zaben tun lokaci da wani gurgu Malam Kabiru Ado Yakasai ya tsaya takarar shugabancin karamar hukuma Nasarawa kuma bai Nasara ba.

Ya ce al’umma sun yadda dashi amma sakamakon rashin iyayen gida haka aka kwace takarar daga hannun sa tare da yi masa alkawarin mukami mai tsoka.

Sai dai bayan da aka ci zabe ko mukamin masinja bai samu ba.

Rashin goyon baya

Malam Shaga yace duk da irin kokarin da masu bukata ta musamman ke yi wajen nuna kansu amma basa samun goyon bayan al’umma.

Ya ce sukan zama abin kallo ko ayi musu dariya ko kyara duk lokacin da suka nuna sha’awar su ta shiga al’amuran siyasa a dama dasu.

“Rashin gwadamu shi yasa mutane suke ganin kamar ba za mu iya ba amma matukar aka bamu dama zamu bada mamaki.

“Tsohon gwamnan jihar Nasarawa Tanko Almakura naga shima wakili ne a cikin kungiyar masu bukata ta musamman ta kasa domin yana fama da lalurar ji.

“Kuma kowa yaga irin kokarin da yayi wajen samun ‘yancin masu bukata ta musamman,” a cewar sa.

 

A don hakan ne ya bukaci al’umma da su dinga zabar masu bukata ta musamman domin suma su nuna tasu kwarewar

Za a basu Fom din takara kyauta

A nasa bangaren shugaban hukumar zabe ta jihar Kano farfesa Garba Ibrahim Sheka ya ce fom din takara kyautane ga duk mai bukata ta musamman.

Sheka ya ce matukar jami’iyyu suka kawo su a matsayin wanda suka ci zaben cikin gida to hukumar za ta basu takarda tsayawa takara kyauta.

Ya ce hukumar tana siyar da takardar tsayawa takarar shugaban karamar hukuma akan N250,000  yayin da kuma takardar tsayawa takarar kasila take siyarwa akan N150,000.

Sai dai ta ce matukar aka kawo su a mtsayin wadanda aka tantance to za ta basu kyauta.

A cewarsa hukumar ta yi hakanne domin ta karfafawa masu bukata ta musamman gwiwa don ganin ana damawa dasu a cikin harkokin siyasa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending