KANUN LABARAI
Sha’aban Sharada ya nemi a rushe ‘yan sandan ‘Anti-daba’ a Kano
Mukhtar Yahya Usman
Shugaban kwamitin tsaro na majalisar wakilai Sha’aban Ibrahim Sharada ya ne me rundunar ‘yan sandan jihar Kano da ta rushe sashin da ke yaki da ‘yan daba da ake kira ’Aniti-daba’.
Kano Focus ta ruwaito dan majalisar ya yi wannan kira ne a ranar Lahadi bayan da ya ziyarci kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano Habu Sani kan kisan da aka yiwa wasu matasa biyu a unguwar Sharada.
Idan za a iya tunawa a shekaran jiya Asabar ne ‘yan sandan Anti-daba suka kashe wasu matasa biyu, ‘yan ba ruwana a unugwar Sharada bayan da sukaje kamen masu laifi.
Matasan da suka hallaka a hannun ‘yan Anti-dabar sune Abubakar Isah da kuma Ibrahim Sulaiman da aka yi ittifakin abokanaine.

Wannance ta sanya al’ummar yankin na Sharada harzuka da kuma fara kiraye-kirayen a soke sashin na Anti-daba.
A cewarsu ko kadan ‘yan sandan na Anti-daba na wuce gona da iri a cikin ayyukan su.
Haka ta sanya Saha’aban Sharada kai koken sa ga kwamishi nan ‘yan sadan na jihar Kano kan daukar matakin gaggawa kan barnar da ‘yan sanda suka yi musamman ma na kashe yan baruwa na.
Cikin bukatar da dan majalisar ya gabatarwa kwamishina shi ne a hukunta wadanda suka yi barnar sannan a gyara musu ayyukan su ko kuma a rushesu ma baki daya.
Yadda al’amarin ya faru.
A cewar mazauna yankin na Sharada, da misalign karfe 11.00 na daren ranar Asabar ne ‘yan sadan na Anti daba suka mamayi yankin dab da masallacin juma’a na Sharada domin kama masu laifi.
Shaidun gani da ido sun ce ‘yan sandan sun mamayi wurin mai sayar da shayi ne da ke kira da ‘Indomie spot’ da suke zargin akwai musu lafi a wurin.
Rikici ya barke ne a dai-dai lokacin da mai wurin Ibrahim Sulaiman ya bukaci sanin dalilin da ‘yan sadan za su kama dan uwansa mai suna Gaddafi duk da cewa ba mai laifi bane.
‘Yan sanda sun kashe matasa biyu a Kano
Budurwa ta kashe kanta a Kano ta hanyar rataya
Rundunar ‘yan sandan Kano ta kubutar da matashi da ya shafe awa 7 a cikin kwata
Sai dai wani dan sanda da ake kira Ado da ya yi yunkurin dakatar da Ibrahim ya yi amfani da wuka inda ya yankeshi har sau biyu.
Hakan ta sanya wani matashi Abubakar Isah da ke wurin ya taso domin kawowa Ibrahim dauki, nan ma wani dan sandan ya sa bindiga ya harbeshi da kuma ya mutu nan take.
A cewar wadanda suka shaida lamarin nan take aka garzaya da su asibiti basa kokarin ceto rayuwar Ibrahim sai dai da misalin karfe 2.00 na dare shi ma ya mutu.
An kama ‘yan sandan
Tuni dai kwamishinan yan sandan jihar Kano Habu A Sani ya bada Umarnin Kama ‘yan sandan da suka yi wannan aika aika.
A cewar Jami’in hulda da jama’a na runduar yan sandan Abdullahi Haruna Kiyawa, Kwamishinan ‘yan sandan ya bada umarnin kama jami’an ne jima kadan bayan da ya samu labarin faruwar al’amarin.
Abdullahi Kiyawa mai mukamin mataimakin sufurtandan ‘yan sanda ya ce ko kadan ba za a bar wannan al’amari ya wuce haka siddan ba.
A cewar sa za a gudanar da bincike za kuma a baiwa mai hakki hakkin sa da zarar an kammala binciken.

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
