KANUN LABARAI
Sha’aban Sharada ya nemi a rushe ‘yan sandan ‘Anti-daba’ a Kano
Mukhtar Yahya Usman
Shugaban kwamitin tsaro na majalisar wakilai Sha’aban Ibrahim Sharada ya ne me rundunar ‘yan sandan jihar Kano da ta rushe sashin da ke yaki da ‘yan daba da ake kira ’Aniti-daba’.
Kano Focus ta ruwaito dan majalisar ya yi wannan kira ne a ranar Lahadi bayan da ya ziyarci kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano Habu Sani kan kisan da aka yiwa wasu matasa biyu a unguwar Sharada.
Idan za a iya tunawa a shekaran jiya Asabar ne ‘yan sandan Anti-daba suka kashe wasu matasa biyu, ‘yan ba ruwana a unugwar Sharada bayan da sukaje kamen masu laifi.
Matasan da suka hallaka a hannun ‘yan Anti-dabar sune Abubakar Isah da kuma Ibrahim Sulaiman da aka yi ittifakin abokanaine.

Wannance ta sanya al’ummar yankin na Sharada harzuka da kuma fara kiraye-kirayen a soke sashin na Anti-daba.
A cewarsu ko kadan ‘yan sandan na Anti-daba na wuce gona da iri a cikin ayyukan su.
Haka ta sanya Saha’aban Sharada kai koken sa ga kwamishi nan ‘yan sadan na jihar Kano kan daukar matakin gaggawa kan barnar da ‘yan sanda suka yi musamman ma na kashe yan baruwa na.
Cikin bukatar da dan majalisar ya gabatarwa kwamishina shi ne a hukunta wadanda suka yi barnar sannan a gyara musu ayyukan su ko kuma a rushesu ma baki daya.
Yadda al’amarin ya faru.
A cewar mazauna yankin na Sharada, da misalign karfe 11.00 na daren ranar Asabar ne ‘yan sadan na Anti daba suka mamayi yankin dab da masallacin juma’a na Sharada domin kama masu laifi.
Shaidun gani da ido sun ce ‘yan sandan sun mamayi wurin mai sayar da shayi ne da ke kira da ‘Indomie spot’ da suke zargin akwai musu lafi a wurin.
Rikici ya barke ne a dai-dai lokacin da mai wurin Ibrahim Sulaiman ya bukaci sanin dalilin da ‘yan sadan za su kama dan uwansa mai suna Gaddafi duk da cewa ba mai laifi bane.
‘Yan sanda sun kashe matasa biyu a Kano
Budurwa ta kashe kanta a Kano ta hanyar rataya
Rundunar ‘yan sandan Kano ta kubutar da matashi da ya shafe awa 7 a cikin kwata
Sai dai wani dan sanda da ake kira Ado da ya yi yunkurin dakatar da Ibrahim ya yi amfani da wuka inda ya yankeshi har sau biyu.
Hakan ta sanya wani matashi Abubakar Isah da ke wurin ya taso domin kawowa Ibrahim dauki, nan ma wani dan sandan ya sa bindiga ya harbeshi da kuma ya mutu nan take.
A cewar wadanda suka shaida lamarin nan take aka garzaya da su asibiti basa kokarin ceto rayuwar Ibrahim sai dai da misalin karfe 2.00 na dare shi ma ya mutu.
An kama ‘yan sandan
Tuni dai kwamishinan yan sandan jihar Kano Habu A Sani ya bada Umarnin Kama ‘yan sandan da suka yi wannan aika aika.
A cewar Jami’in hulda da jama’a na runduar yan sandan Abdullahi Haruna Kiyawa, Kwamishinan ‘yan sandan ya bada umarnin kama jami’an ne jima kadan bayan da ya samu labarin faruwar al’amarin.
Abdullahi Kiyawa mai mukamin mataimakin sufurtandan ‘yan sanda ya ce ko kadan ba za a bar wannan al’amari ya wuce haka siddan ba.
A cewar sa za a gudanar da bincike za kuma a baiwa mai hakki hakkin sa da zarar an kammala binciken.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Hausa
Rabiu Chanhu: Dan wasan da ya hada kwallon kafa da karatu

Jamilu Uba Adamu
Da yawan masoya da mutanen dake bibiyar wasan Kwallon Kafa, a Arewacin Najeriya, musamman Jihar Kano ba su cika tsammanin akwai alaka tsakanin ilimi da wasan Kwallon Kafa ba.
Kasancewar a lokuta da yawa matasan dake buga wasan Kwallon Kafa basu cika samun nasara a makaranta ba, ko samun damar yin karatu mai zurfi ba.
Amma sai dai kamar yadda bincike ya nuna, ‘yan Kwallo da yawa a fadin duniya har ma da nan gida Najeriya sun samu daukaka mai yawa a bangarorin ilimi.
A misalin irin wadannan ‘yan kwallo akwai; Socrates na Brazil, wanda yazama Dakta. Anan gida Nijeriya akwai irin su Sir, Segun Odegbami.

Anan gida Jihar Kano kuwa, Allah ya yi mana baiwar samun wannan bawan Allah da zan kawo sharhi da takaitaccen tarihinsa, musamman akan wasan kwallon kafa.
Don saboda ya zama madubi abun dubawa ga na baya, musamman wajen hada wasannin motsa jiki da neman ilimin addini da na boko.
Rabiu Chanhu ya fara buga kwallo ne a karamin kulab mai suna Silver Stone dake unguwar Kofar Mazugal. Kuma ya yi wasanni ne na makaranta a lokacin yana karatu a makarantar sakandiren horas da malamai ta garin Bichi, inda daga nan ne Kungiyar Kwallon Kafa ta Super Star dake unguwar Makwalla ta cikin birni ke dauko shi a matsayin sojan haya dan ya buga musu wasa.
A irin wannan wasannin ne ya taimakawa Kungiyar Kwallon kafar ta Super Star samun nasara lashe gasar kofin Dan’wawu wadda ita ce mai daraja ta daya a jihar Kano a wannan zamanin.
Wanda ganin irin bajintar da kwarewar da ya nuna a wannan wasan ne yasa Kungiyar Kwallon Kafa ta Raccah Rovers ta dauke shi dan ya buga Mata wasa a shekarar 1981, kuma ta yi masa rijista.

Farfesa Rabiu Chanhu
A wancen zamanin shi da Abubakar Zagallo (yanzu shine na’ibin limamin masallancin Juma’a a wata Unguwa a New York, America) su ne suke buga lamba biyar da shida a bayan kungiyar kwallon kafa ta Raccah Rovers.
Tsohon dan wasan Kwallon kafar, ya canja sheka daga Raccah Rovers zuwa kungiyar kwallon kafa ta Bank of the North, bisa kin yarda da ya yi da cigaba da bugawa Raccah Rovers wasa bayan kungiyar ta chanja suna zuwa Nigerian Breweries.
Wanda kamar yadda ya bayyana min cewar hakan yana da nasaba da addinin sa na muslunci. Kuma tare da marigayi Usman Danlami Akawu Kofar Wanbai, Wanda shi ma shaharren dan wasan kwallon kafa ne (Allah ya gafarta masa. Ameen) suka koma kungiyar Bank of the North.
Ya ajiye takalmansa na wasan kwallon kafa ne a shekarar 1989. Sai dai kuma ya yin da yake karatunsa na master’s a jami’ar Bayero, an zabe shi a jerin Wanda zasu wakilci kasa Najeriya a gasar Jami’o’i ta Duniya a wasan Kwallon Kafa a shekarar 1995.
A zamanin da Professor yake taka wasa, saboda kwarewarsa a wasan ya samu sunayen inkiya daban-daban wanda ‘yan kallo suka lakaba masa. Sukan kira shi da Na Makwalla, Chanhu, Maigida a sama.
Yanzu dai haka, Malam Muhammad Rabiu “Chanho” Professor ne a Wanda keda kwarewa a ‘adopted physical education’, bangaren Kinetics and Health Education dake Jami’ar Bayero, Kano.
Jamilu Uba Adamu
Mai bibiyar Tarihin wasanni kwallon kafa ne. Za a iya samunsa a +234 803 207 8489
