Connect with us

KANUN LABARAI

Ranar yaki da cin zarafin mata: Yadda mata a Kano ke rayuwa cikin ukuba

Published

on

Zulaiha Danjuma

A ya yin da ake bikin ranar yaki da cin zarafin mata ta duniya,  mata a nan Kano sun bayyana yadda suke rayuwa cikin ukuba a gidajen miji da kuma cin zarafinsu akan hanya da makarantu,  da kuma yadda dangi ke nuna musu wariya.

A zantawar Kano Focus da wasu mata a nan Kano sun ce rayuwarsu a gidan miji sai godiya, domin kuwa ba ta da maraba da rayuwa akiyama.

Ya yin da wasu kuma suka ce rayuwa a gaban iyayensu da sauran danginsu ita ke zame su ukuba.

Haka zalika wasu matan sun ce suna fuskantar cinzarafi a kan titi, ta yadda maza ke hantarasu yadd suka ga dama.

Matsalolin aure

Rabi’utu Abba uwa ce da ke da yara uku ta shaidawa Kano Focus irin rayuwar ukubar da take fuskanta a gidan mijinta, musamman ma daga bagaren danginsa.

Ta ce har yanzu tana iya tuna yadda dangin mijinta suka yi mata taron dangi wajen zaneta.

“A wata ranar Asabar a watan Fabrairun shekarar 2015 mun tsara cewa a ranar litinin mai zuwa ne za mu fara kai yaranmu makaranta, sai ga yan uwan sa sunshigo da zagi da cin zarafi da barazanar sai sun koreni daka gidan.

“Kafin na ce wani abu kanin mjina ya sureni ya kuma damfarani da kasa, kafin kace kwabo sauran sun rufeni da duka

“Wani abin takaici da ke sosa raina har yanzu shi ne da mijina ya zo kawai sai ya goya musu baya, tundaga wannan rana naji sansa ya fita a raina, a na dai zaman ne kawai” A cewarta.

Hafsat Sani wata daliba ce da ke karatu a jimi’ar Bayero ta shaidawa Kano Focus irin yadda ‘yar uwarta ke karbar ukuba a gidan miji.

A cewarta ‘yar uwarta ta auri wani malamin makaranta a jami’ar Bayero da dake  azabar neman mata.

“Abinda zai baka haushi shi ne yadda yake neman matan da basu cika manta ba a jama’ar, ya kuma yi musu barazana da zai kayar da su idan basu amince da shi ba.

Zaben kananan hukumomi: Matashi ya sha fiya-fiya kan dan takara a Kano

Gwanda yawo a kwararo da zaman ukubar gidan miji- matar aure

Ranar bandaki: Yadda matsalar bandaki ke tagayyar dalibai mata a makarantun Kano

“Sanna matar nan ta san dukkanin masha’ar da ya ke aikatawa, amma dai ta ci gaba da zama da shi.

“Dukan tsiya ya ke mata kullum, kuma duk sanda ya dake ta sai ta suma, sannan, yana tsaka da dukan nata zai fara nemanta, yana nemanta yana dukanta.

“Haka kuma baya basu abinci har ma yaran da ya Haifa, amma haka take zaune da shi, sai dai ta bi dangi menam me za su ci.

Ita kuwa wata mata mai suna Esther da ke unguwar Nasarawa a nan Kano ta shaida yadda take shan azaba a hannun mijinta.

Ta ce mijnta na dukanta kowacce rana ba tare da la’akari da lafiyarta ba.

Ta kara da cewa bayan da ta kai kara wajen mahaifiyarsa sai ta ce mata, sai dai ta yi hakuri haka suka yi gadon duka, shima a wurin ubansa ya gada.

Ta ce a yanzu haka gudawa ta ke cikin wata makarantar firamare a nan Kano tana kwana, alabashi da safe sai ta koma gidan.
Auren dole

Zahra Auwal, daliba ce da ke karantar aikin likita a jimi’ar Bayero ta ce mahafiyarta ta tsaneta saboda ta ki auren wani mai kudi da uwar keso ta aura.

A cewar ta hakan ta sanya baya ga tsanar da uwar ta yi mata dangi ma suka sawo ta a gaba.

Ta ce ta shiga damuwa da tashin hankali kan yadda kowa ya tsaneta saboda taki auren mai kudi, a cewarta shekaru hudu ke nan tana cikin wanna bala’i.

“Loacin da nake tasowa babana yana son na yi karatu, haka kuma ya sanyamin son karatun.

“Masu nemana da yawa sun fito amma sai yace musu a bari na kammala karatuna, sai da na gama sakandire ne kuma wani yafito nemana da aka dameni na aurenshi.

“A lokacin shekaruna 16 ina so na ci gaba da karatu, shi kuma irin  mutanen nan ne da kasuwace kawai a gaban su ba karatu ba.

“Naki na aureshi ne, kan wannan dalili, amma da yake yana da abin hannu sai ya rufewa dangina ido.

“Mahaifiyata ta tsaneni saboda naki na aureshi, a yanzu da nake karatu a jami’ar Bayero har fargarbar komawa gida nake idan anyi hutu saboda kalubalen da zan fuskanta.

Cin zarafin akan hanya 

Wasu matan da Kano Focus ta zanta da su sun shaida irin tasu matsalar da cewar ana cin zarafin su ne akan hanyoyi, musamman ma a cikin kasuwanni.

Zainan Nasiru wata budurwace a nan Kano ta ce ta sha gamuwa da barazana da cin zarafi daga maza.

Zainab ta ce a yanzu haka tana tsoron shiga jama’a ne saboda cin zarafin da ta fuskata.

“Lokacin ina daliba a jami’ar Bayero an kafe sakamakon jarrabawa, mun taru muna dubawa, sai kawai wani yazo ya tsaya a bayana, kamar yana duba nasa sakamkonne, kawai sai ya fara shafani a mazaunaina.

“Na yi zaton cinkonson jama’ ne ya saya ya matseni haka, sai nayi kokarin canza wuri, amma makirin sai ya biyo ni ya ci gaba da shafani har ya kai min hannu kasan.

Dole ne manyan makarantu su bi doka wajen yaki da cutar Covid-19 a Kano-Kwamish

Dalilan da ke sa iyaye yiwa ‘ya’yansu auren dole

‘Yan wasan Hausa a Kano sun yi tofin alatsine ga shugaban Faransa

“Da na fuskanci hakan ne sai na kwalla ihu domin ankarar da jama’a a binda ya ke yi , amma sai ya yi mursisi ya ce shi ko kadan bai aikataba.

“abin takaicin shi ne yadda jama’ar wurin suka goyamasa baya suka nuna ai ma sharri nake son yi masa, lallai wanna cin zarafi ne babba.” A cewar Zainab.

Ita ma wata Fatima Ahmad ta ce cin zarafin da ta fuskanta a cikin kasuwar kantin kwari ne.

Ta ce ta ziyarci kasuwar ta kwari da wasu mata uku domin yin siyayya sai kawai suka fada cikin wani cinkoso.

“Shiga ta cikin wannan cinkosonne sai na ji wani matum na gogamin gabansa a bayana.

“Ba shirin na daskare a wurin saboda tsoro, saboda ban taba fuskantar irin hakan ba.

“Bayan farfadowa daga razanar da nayi ne, sannan na ci gaba da kwarara ihu.

“Kafin a ankara ya bi cikin taron jama’a ya bace sanan na dawo gida na shiga na yi wanka.

“Tun daga wannan rana ban kara zuwa kasuwa ba sai na nemi katuwar jaka na rufe mazaunaina da shi, guduna sake fadawa cikin wannan masifar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Trending