KANUN LABARAI
Satar yaran Kano 118: Iyayen yaran sun zargi gwamnati da nuna halin ko inkula
Aminu Abdullahi
Yayin da aka cika shekara goma da fara satar yara a Kano ana kaisu kudancin kasarnan, iyayen yaran sun zarigi gwamnatin Kano da nuna halin ko inkula wajen kubutar da yaran nasu.
Kano Focus ta ruwaito wannan zargi na fitowa ta bakin wasu daga cikin iyayen yaran mata lokacin da suke gudanar da zanga-zangar lumana kan sace yaran nasu ranar Alhamis a nan Kano.
A cewar jagorar masu zanga-zangar Aisha Haruna Kabuga haryanzu suna cikin wani hali na rashin dawo musu da yarannasu.
Ta ce kwamitin da gwamnati ta kafa kusan shekara guda da watanni ya gaza tabuka wani abun kirki.

“Ko yaushe muka tuntubi kwamitin sai suce mu saurare su suma suna sauraren gwamnatine.
“Gwamna ya gayyace mu, kuma batun yana gaban kotu amma har yanzu shiru ba abinda akayi,” a cewar ta.
Aisha ta kuma yi kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da Gwamnan Kano Abdullahi Umar Gabduje da suyi duk mai yiwuwa don kubutar musu da yaransu kamar yadda aka kubutar da yaran jihar Katsina.
Ta ce a cikin yara 118 da suke nema har yanzu ba suga yaro ko guda dayaba.
“Mun kasa yadda cewa gwamnati na yin wani abu don a kwato mana yaranmu kuma ansan inda suke.
“Mun zama kamar bamuda shugabanni, kamar bamuda manya a arewa, saboda ba ‘ya’yansu aka sace ba,” a cewar ta.
Ita ma wata uwa Zainab Abdullahi Giginyu cewa tayi watanni uku da suka gabata sanatan Kano ta Kudu Kabiru Gaya ya ce an gano wasu daga cikin yaran sai dai har yanzu basu ga ko daya ba.
Itama Aisha Bashir ‘Yankaba ta ce akwai ‘danta mai suna Musa Abdurrauf da aka ganoshi a jihar Anambra, sai dai har yanzu an gaza dauko shi.
Ta ce ko a cikin yaran da aka debo Aisha da Farouk sun tabbatar mata da cewa makaranta daya aka sakasu tare da dan nata a can Anambra.
“Abokinsune kuma sun tabbatar min dacewa yana can amma gashi gwamnati ta watsar da al’amarin ba tama kulawa da halin da muke ciki.
“Shekaru shida kenan da sace min yaro, ya kamata gwamnati ta san cewa danmu take yin mulkin nan,” a cewar ta.
Da take mayar da jawabi, kwamishiniyar mata da walwalar kananan yara ta jihar Kano Zahra’u Muhammad Umar ta ce gwamnatin Kano ta shirya tawaga da za ta nemo yaran da aka rasa.
Ta ce rikicin zanga-zangar Endsars da bullar annobar Korona ne ya dakatar da tafiyar.
Ta kara da cewa dole ne aji shiru daga kwamitin da gwamnati ta kafa don dawo da yaran, domin abu ne da ya shafi tsaro da ba za a dinga bayyana duk shirye shiryen da ake yi ba.

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
