Connect with us

KANUN LABARAI

Yadda na haihu cikin yashi da duwatsu a asibitin AKTH-Mai jego

Published

on

Zulaiha Danjuma

Wata mata mai suna Hafsat Uzairu ta ce ma’akatan Asibitin koyarwa na Aminu Kano sunci mutuncinta lokacin da taje haihuwa, da hakan ya sa ta haihu a cinkin yashi da duwatsu.

Kano Focus ta ruwaito matar ta haihune da asubahin ranar Alhamis bayan da ma’aikata dakin karbar haihuwa na asibitin suko korota waje a dai-dai lokacin da ta ke nakuda.

Ta ce ma’aikatan sun mata wulakanci mai tsanani da ba za ta taba mantawa da shi a rayuwartaba.

“Banji dadin abun da ya faru ba, sun wulakantani, sun koreni cikin dare suka ce in 2cm in fita basa karbar wadanda ke a 2cm.

“Fitowata kenan kawai na haihu a cikin yashi da duwatsu” A cewarta

Aikin Hukumar Anti-corruption ta Kano ya yi awon gaba da kwamishinoni da daraktoci -Ganduje

Dakarun tsafta 1000 a Kano sun nemi a mayarda su ma’aikatan din-din-din

NMA ta yi korafi kan karancin likitoci a Kano

Haka zalika shima miji ga matar Malam Muhamad ya ce ko kadan ba zai kyale wannan wulakancinba zai kuma nemi hakkin matarsa da aka ketawa haddi.

“Tun daga bakin kofar shiga dakin haihuwa aka fara yi mana wulakanci.

“Sun korota daga ciki suka ce ai a 2cm take su ba za su iya karbarta ba suka korota waje.

“Da zuwanmu da haihuwarta baifi minti 5 ba, a cikin yashi, a yashin da yake gaban dakin haihuwa” A cewarsa

Kokarin jin ta bakin mahukuntan asibitin kan al’marin ya ci tura, tun bayan da aka nemesu kuma ba a samesu ba..

Sai dai da Kano Focus ta tuntubi jami’ar hulda da jama’a ta Asibitin Hauwa Abdullahi, inda  ta ce za ta nememu ta yi mana karin bayani, sai dai har lokacin hada wannan rahoto ma muji daga gareta ba.

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Hausa

Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.

Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.

Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.

A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.

Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Continue Reading

Hausa

Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.

Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.

Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.

A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.

Continue Reading

Trending