KANUN LABARAI
‘Yan Vigilante sun kama wanda ke labewa a kwana yana kama ‘yan mata
Aminu Abdullahi
Jami’an Vigilante sun kama wani magidanci mai suna Ibrahim da ke zaune a unguwar yan awaki a karamar hukumar Tarauni, bisa zargin labewa a kwana yana cakumar \yan mata, da matan aure.
Kano Focus ta ruwaito cewa an kama wanda ake zarginne mai ranar Litinin bayan daya dakumi mazaunan wata matar aure, lokacin da ta ke tsaka da tafiya.
Matar auren da ta nemi a sakaye sunanta ta ce tana cikin tafiya kawai sai wanda ake zargin ya biyo ta bayanta a dakume mata mazaunai. A cewarta ta yi tunani zai kauce ne ya bata hanya ko kuma ita ta kauce masa amma sai kawai taji ya aikata wannan barna.
“Ji nayi kawai an rikemin mazaunai, sai ya wuce da ya yi gaba sai yaga maza ya yi tunanin zanyi masa ihu sai ya dawo sai nace masa Allah ya yarda sai anyiwa ‘ya’yan shi shine ya ce nayi hakuri.
“Ashe yana biye dani dazan dawo ma sai na sake ganin sa har ya canza hanya sai ya sake biyowa inda nake shi ne nace masa sake yimin zakayi to wallahi ka tabani kagani shi ne ya wuce baice komai ba,” a cewar ta.
Jami’an Vigilante a Kano sun kama barawon baburin Opay na zuwa burge ‘yan mata
‘Yan Vigilante sun kama dilan kwaya a kasuwar ‘yan Kaba
‘Yan daba sun kone gida jami’in Vigilante tare sassara kwamadansu a Kano
Itama wata matar aure ta ce wanda ake zargin yana sanya takunkumin rufe fuska don kada a gane shi, wasu lokutanma sai a yi zaton wani yake jira.
Ta kara da cewa ya dauki lokaci mai tsayi yana yiwa matan dake wucewa barazana musammanma idan rana tayi yayin da mazajen yankin suka fita neman abinci.
A nasa bangaren wanda ake zargin Ibrahim Isma’il mazaunin unguwar Hotoro Tsamiyar Boka ya ce a kalla ya kaiwa mata guda biyar hari.
A cewarsa ya shafe watanni biyu yana aikata muguwar ta’adar tasa, ya kara da cewa duk da yana da aure amma karfin sha’awane yasa shi aikata haka.
Kwamandan ‘yan Vigilante dake ‘Yan awaki mai suna Adamu Abubakar Fiya-fiya ya ce sun shafe watanni uku suna farautar wanda ake zargin,
Amma sai a wanna lokaci Allah ya basu damar kamashi.
Ya ce akwai matan da suka kawo musu korafin cewa yana taresu tsakanin bayan masallacin juma’a na ‘Yan awaki zuwa wani layi dake bayan wata makaranta mai zaman kanta a unguwar.
“Mun kamashi kuma zamu mika shi hannun hukumar Hisbah don girbar abinda ya aikata,” a cewar sa.
Hausa
Mutane 18,000 sun amfana da aikin ido kyauta ta Gidauniyar Mangal a Katsina
Kimanin marasa lafiya masu rauni 18,000 da ke fama da cututtukan ido daban-daban a jihar Katsina sun amfana da ayyukan kulawar ido da tiyata kyauta da Gidauniyar Mangal ta dauki nauyi tun bayan kafuwarta a shekarar 2016.
Wani mamba na kwamitin amintattu (Board of Trustees) na gidauniyar, Malam Hussaini Kabir, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin kaddamar da aikin tiyatar ido na zangon karshe na shekarar 2025 a Cibiyar Ido ta Katsina.
Kabir ya bayyana cewa kimanin mutane 7,000 ne suka amfana a shekarar 2025 kadai, daga sassan jihar Katsina, jihohin makwabta, har ma da wasu yankuna na Jamhuriyar Nijar.

A cewarsa, gidauniyar ta fara tantance wadanda za su amfana kimanin makonni biyu da suka gabata, inda marasa lafiya da dama suka samu magunguna kyauta da tabarau na likita.
Kabir ya kara da cewa wadanda ke bukatar tiyata an dauki nauyin dukkan zaman asibitinsu gaba daya, yana mai cewa kimanin marasa lafiya 2,000 aka tantance a yayin aikin zangon karshe da ake ci gaba da yi.

Ya sake jaddada kudirin gidauniyar na inganta samun kulawar lafiya, yana bayyana shirin a matsayin wani bangare na nauyin alhakin zamantakewar kamfanoni (corporate social responsibility).
“Manufarmu ita ce tallafa wa kokarin gwamnati tare da rage nauyin kudin kula da lafiya ga mafi rauni, musamman wadanda ke fama da matsalar biyan bukatun rayuwa,” in ji shi.

Wani likitan ido a cibiyar, Dokta Ahmad Hamza, ya bayyana cewa an gano marasa lafiya da dama na fama da cutar idon toka (cataract) da glaucoma, cututtuka da galibi ke bukatar tiyata.
Ya jaddada muhimmancin duba ido akai-akai, yana mai cewa gano cuta da wuri na taimakawa wajen hana asarar gani ta dindindin da cututtukan ido masu zuwa a boye ke haifarwa, kamar glaucoma, cataract da lalacewar macula (macular degeneration).

Daya daga cikin wadanda suka amfana, Malam Yusufa Usman, ya ce ya shafe sama da shekaru biyu yana fama da matsalar gani amma ba shi da ikon biyan kudin tiyata.
“Tsawon shekaru biyu ban iya gani sosai ba, amma yau na yi tiyata kuma ina da fatan ganina zai dawo.
Ina rokon Allah Madaukakin Sarki ya saka wa Gidauniyar Mangal da alheri bisa wannan kyakkyawan aiki.
“Ina fatan sauran masu kudi za su yi koyi da wannan abin a yaba,” in ji Usman.

Wata mai amfana, Aisha Muntari daga kauyen Bakuru, ta bayyana kwarewarta yayin da take jiran a kai ta dakin tiyata.
Muntari ta ce ta kamu da matsalar ido kimanin shekara guda da ta wuce kuma ta kusa yanke tsammani kafin ta samu labarin shigar gidauniyar, tana mai bayyana kwarin gwiwar cewa nan ba da dadewa ba ganinta zai dawo.
Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano
Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”
Hausa
Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye
Nasiru Yusuf Ibrahim
Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.
Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.
Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.
Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.
A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.
Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.
