KANUN LABARAI
Da a gina masallatai da islamiyyu gwanda a zuba kudin a harkar film-Aminu Momo
Aminu Abdullahi
Fitaccen jarimin masana’antar Kanywood Aminu Saharif Momo ya ce Ya ce a yanayin da ake ciki yanzu da a gina masallatai da islamiyyu gwara a zuba kudaden a harkar shirya fina-finan hausa.
Kano Focus ta ruwaito Momo ya bayyana hakan ne cikin shirn ‘Barka da hantsi’ na gidan rediyo freedom da safiyar yau Laraba.
Ya ce zuba kudaden a masana’antar ta kanywood sadaka ce mai gudana da za a amfana ana duniya da gobe kiyama.
MOmo ya kuma yi kira ga mawadata da su dinka tallafawa masana’antar ta Kannywood da kudade kamar yadda suke tallafawa marayu da sauran masu bukata ta musamman.

Momo ya ce al’umma za su iya zabar irin fina-finan da suke so ayi musu da suka shafi al’ada da dabi’un malam bahaushe matukar za su dinga bada tallafin kudade ga masana’antar.
Ya kuma ce ya cancanta a rinka fitar da kudade daga cikin tsarin zakka da za a rinka shirya fina-finan hausa da sauran shirye-shirye domin jama’a su amfana.
Ya ce duk wanda ya zuba kudinsa a harkar fim tamkar yayi sadakatul jariya ne don kuwa ladan zai bishi har zuwa kabarinsa matukar za a dauka a kalla to zai samu lada a cewar sa.
Matsalar tsaro: ‘Yan wasan Hausa a Kano na caccakar shugaba Buhari
Hausa fim: Yaron da yazo Kano daga Adamawa don ganin Ado Gwanja
‘Yan wasan Hausa a Kano sun yi tofin alatsine ga shugaban Faransa
Ya kara da cewa ko a baya anyi gwamnatotcin da suka bada kudade wanda aka shirya fina-finai kanana ta karkashin hukuma don tattare fina-finan da basu da kyau.
“Yana da kyau a dawo da wannan tsarin gwamnati da al’umma su fito da wadannan kudade.
“A nemi masu shirya fina finai ai tayi ana tura su kafofin sadarwa don toshe irin wandancan marasa kyau.
“Mun ga yadda ake tura wa’azuzzukan malamai kuma wasu suna fadakarwa, to idan aka dauki wannan salon aka rinka shirya wadannan fina-finan to za su taimaka matuka,” a cewar sa.
Ya kara da cewa yakamata a dunga yiwa al’umma kyakkyawar fahimta ta yadda za a samu gyara ya ce akwai nauyi akan attajiran mu da su rinka fitar da zakkarsu ga masana’antar shirya fina finan hausa.

Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

Hausa
Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Nasiru Yusuf Ibrahim
Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.
Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.
Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.
A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.
Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Hausa
Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Nasiru Yusuf Ibrahim
Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.
Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.
Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.
A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.
