KANUN LABARAI
Ayi muku kayan daki, ayi muku gara, kuce a soke lefe-martanin ‘yan mata ga samarin Kano
Aminu Abdulahi
‘Yan mata da dama ne suka soki kiran shehin malamin nan na Kano Sheik bn Usman na cewar lokaci ya yi da yakamata a soke lefe.
Ya yin zantawar Kano Focus da wasu ‘yan mata a Kano sun nuna rashin amincewarsu karara da wancan kira na malamin, ko da dai wasu sun ce maganar malamin akwai kanshin gaskiya.
Sun ce mlamai basa kulawa da bukatun bagaren mata, ko da yaushe sun fi kula da al’amuran da suka shafi maza.
Suka kara da cewa ana yiwa maza kayan daki a kuma yi musu gara idan za su auri mace, amma ba wanda ya ke cewa a soke wadannan sai dai a soke lefe.

Idan za a iya tunawa dai a rana juma’ar da ta gabata yayin tafsirin alqur’anin da yake gabatarwa a masallacin Sahaba deke kundila sheikh bn Usman ya ce lokaci ya yi da yakamata a soke lefe.
Malamin ya ce al’adar yin lefe ta zamewa samarin da ke da niyyar yin aure kadangaren bakin tulu, biyo bayan tsarebe-tsaraben da ke cikinsa.
Ya ce ba yana inkarin al’ada bane sai dai kar al’ada ta shigo da wahalarwa.
Ya kara da cewa al’ada na saka mutane shiga cikin damuwar da ta ke sanyasu siyar da kadarorinsu.
Kiran ya sosa zucuyar ‘yan mata
Sai dai wannan kira da jan hankali bai yiwa ‘yan mata da dama dadi ba, inda galibinsu suke ganin kamar malamin na son jawo musu jangwamne.
Haka zalika wasu ‘yan matan sun yiwa zance malamin karatu na tsanaki inda suka ce akwai kanshin gaskiya a bukatar da ya bijiro da ita.
Mata za su iya tafiya tsirara
Suwaiba Isma’il Gadon Kaya cewa tayi a wannan zamanin da wasu mazan ke da rashin kulawa ga matayensu idan aka soke lefe sai wata matar ta tafi tsirara.
Ta ce wani namijin idan yayi lefe yana shekara biyar bai dinkawa matarsa koda dankwali ba.
“Abin takaici sai namiji ya dinga bin matan waje wai saboda su fes suke, shima tasa ta gidan da zai bata kulawa fes zai ganta.
“Kullunm magana daya malamanmu suke, shi ne marwa jinsin maza sauki amma basa nemawa jinsin mata sauki a aure.
“Mai yasa basa kira ga iyayen yarinya da su dena kayan ɗaki, mazan su dingayi, meyasa basa kira da adena yiwa maza gara su mazan su tanadi kayan abincin.
Maza na anfanuwa da lefe
Ta kuma ce lefen ba iya mata yake taimakawaba har da maza domin ba gidansu matan suke kaiwa ba.
“Wasu abubuwan ma aciki tare zakuyi amfani dasu, kamar mayuka da turaruka.
“Su kuwa iyayenta gara suke daukowa daga gidansu su kawo maka gidan ka,” a cewar Suwaiba.
Khadija Abba Garba dake unguwar Sheka ‘Yar Kasuwa ta ce soke laifen zai sa maza suki daukar aure da mahimmanci.
Rashin lefe zai haifar da sakin mata cikin sauki
Khadija ta kara da cewa lefene ke kara armashin aure, in kuwa har akayi aure ba tare da lefe ba maza za su cigaba da sakin matansu cikin sauki.
Haka kuma zai basu damar yin auri-saki saboda ba za su sha wahalar lefe.
“Za kaga yanxu koda wasu sunaso su saki matansu, zakaji suna cewa yanxu in zan kara aure sai na kuma yin wahalar lefe.
“Ni a ganina wannan batun nasa baiyi ba saboda maza za su dau mata a arha”
“Amma kuma rashin yin lefen shi zai sa maza su ringa yin aure da wuri, sai dai ba zai dinga yin karkoba, kuma ma idan maza sunyi lefen ai su a kewa ado da kayan,” a cewar ta.
Soke lefe zai kawo raguwar zinace-zinace
Binta Garba Makwarari ta ce lefe ya zama tashin hankalin aure a yanzu musamman ma idan wanda zai yi aure bashida hanyoyin samun kudi yadda yakamata.
Ta ce baiwa maza sauki wajen yin aure zai kawo raguwar zinace-zinace da doguwar soyayya.
“Wallahi da za a hakura da lefe da anji dadi a harkar aure.
“Zinace-zinace da doguwar soyayya kafin aure da duk sun yi karanci.
“Sannan duk kokarin da gidan angwaye za su yi su kai wannan lefen idan ba a yi da gaske ba sai an kushe.
“Ya ilahi ina zamu kai dogon buri a rayuwa.” A cewar ta.
Ta kara da cewa sadaki kwakkwara yafi lefe tana mai cewa kamata yayi a dinga duba aure a matsayin ibada fiye da nishadi.
Hadiza Yusuf ta ce inda za a bar yin lefe sai anfi zama lafiya tsakanin ma’aurata.
Ta ce dayawan dangin amarya kan zuba ido don ganin lefen da za a kawowa ‘yar su wanda idan bai yi musu ba sai su raina.
“Haka dangin ango dashi kansa angon kan zuba idon ganin me aka zuba adaki, idan baiyiba suma su raina, har ana zuba idon ganin alakoron gara daza a lodo itama rainawa ake daga nan ake fara samun rashin zama lafiya da gori,” inji Hadiza.
Yin lefe ke sa maza rike matansu.
Umar Abubakar wani matashi a nan Kano ya ce baya goyan bayan soke lefe dan kuwa da yawan maza sunfi rike matansu ne la’akari da kudaden da suka kashe yayin auren.
Ya ce idan har aka soke lefe to maza za su cigaba da yiwa aure rukon sakainar kashi, da haka zai sa a cigaba da samun mutuwar aure a kasar hausa.
“Duk abinda aka fada hakane amma maganar gaskiya wasu mazan na yanzu mafi yawansu basa mutunta aurensu.
“Sai namiji ya kashe makudan kudi ya narka lefe nagani na fada amma daga anyi auren sai ya dinga wulankanta matar to yayi lefen kenanfa ina kuma ga baiyi ba.
“Gani zaiyi sadaka aka bashi yana da damar da zai wulakanta yar mutane aganin sa,” a cewar sa.

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
