KANUN LABARAI
Gwamnatin Kano ta musanta rushe gadar Kofar Nasarawa
Mukhtar Yahya Usman
Gwamnatin Kano ta ce ko kadan bata da shirin rushe gadar Kofar Nasarawa illa iyaka wasu yan gware-gyare da za yi a jikin gadar.
Kwamishinan yada labarai na jihar Kano Malam Muhammad Garba ne ya bayyana hakan ta cikin shirin ‘Barka da hantsi’ na gidan rediyo freedom ranar Litinin.
Muhammad Garba ya ce ko kadan ba a ce za a rushe gadarba, illa iyaka gyare-gayare da aka ce za a yi a jikin gadar da ake ganin tana bada barazana.
Ya ce, ya yi bayani ne a baya kan halin da gadar ke ciki, inda ya ce masana na nan na hada bayani kan halin da gadar ke ciki, na matsalolin da ake ganin ta samu.

Garba ya ce da zarar sun karbi sakamakon binciken, za su yi amfani da bayanin wajen gyara duk abinda suka bijori da shi.
Idan za a iya tunawa dai, tun a ranar Taladar da ta gabata ne Muhammad Garba ya ce akwai yiwurar rushe gadar sama ta kofar Nassrawa sakamakon zaizayerar da ta fara yi.
Muhammad Garaba ya sanar da hakan ne lokacin da yake karbar kungiyar ‘Ganduje raya Kano yake’.
Ya ce, tuni suka shiga nazari tare da ƙwararru kan irin matsalolin da gadar ke haifar wa ga al’ummar Kano.
Ya kara da cewa gadar ta fara zaizayewa saboda rashin kyawun aikin da aka yi, tana kuma hada cunkoso.
Kwamishinan ya ce, da zarar ƙwararru sun gama nazari a kai, gwamnati za ta duba yiwuwar rushe gadar tare da sake ta.
Sai dai kwamishinan ya ce jama’a basu fahinci abinda kalaman nasa ke nufi ba.
Ya ce za su yi aiki ne da bayanan kwararru, da kuma shawarar da suka bayar, idan ma takama a rushe wani bangare na gadar domin a yi gyara to za a rushe, amma ba rusheta baki dayaba.

Hausa
Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Nasiru Yusuf Ibrahim
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.
“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.
“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.
“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.
“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

Hausa
Zan ɗora ƙaramar hukumar Nassarawa kan manufofin jagoran Kwankwasiyya – Ogan Ɓoye

Nasiru Yusuf Ibrahim
Ɗan Takarar Shugabancin Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jam’iyyar NNPP Amb. Yusuf Imam Ogan Ɓoye ya yiwa jama’arsa godiya kan goyon bayan da suke nuna masa.
Ogan Ɓoye ya ce yayi farin ciki matuƙa da irin goyon bayan da ya samu a lokacin da yake yaƙin neman zaɓe.
Ya yi alƙawarin cewa zai yi iya ƙoƙarinsa idan ya yi nasara a zaɓe wajen ciyar da ƙaramar hukumar gaba.

Ya ce, zai ɗora ƙaramar hukumar kan manufofin jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso na gina rayuwar talakawa ta hanyar inganta ilimi lafiya da tattalin arziki.
A ƙarshe Ogan Ɓoye ya yi kira ga jama’ar ƙaramar hukumar su fito ƙwansu da kwarkwata ranar zaɓe don kaɗa masa ƙuri’a.
Ogan Ɓoye dai na cikin fitattun jagororin matasan Kwankwasiyya da suka yi suna wajen tallafawa matasa ƙarfi.

Hausa
Ruwan sama na barazanar raba hanyar Dawakin kudu zuwa Tsakuwa

Nasiru Yusuf Ibrahim
Mamakon ruwan saman da ake yi a ‘yan kwanakin nan na barazanar raba hanyar da ta tashi daga Dawakin kudu zuwa garin Tsakuwa.
Wani mazaunin yankin Malam Umar Musa Aliyu Dukawa ya ce zaizayar ta shafi gadar fansallah ne dake Maishudi kan hanyar zuwa garin Tsakuwa.
Malam Musa ya ce a baya ma wurin ya taba riftawa, mutanen garin Tsakuwa suka yi gangami suka gyara.

Ya kara da cewa tsohon dan majalisar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Dawakin kudu da Warawa Hon. Mustapha Bala Dawaki ya taba gyara hanyar.
A don haka ya ce akwai bukatar hukumomi su kawo dauki don gyara hanyar kafin ruwan sama ya raba ta biyu.
