Connect with us

Hausa

Yadda Abdullahi Abbas ya sa aka kona ofishin mu-Barau Jibril

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

Sanatan Kano ta Arewa Barau I Jibrin ya zargi shugaban jam’iyyar APC tsagin gwamnan Kano Abdullahi Abbas da kona masa ofishi.

Haka kuma sanatan ya zargi  shugaban karamar hukumar Gwale, Khalid Ilyasu Diso da kuma mataimaki na musamman ga gwamnan Kano kan al’amuran na musamman Murtala Gwarmai  da hannun a ciki.

Mai magana da yawun Sanata Barau, Shitu Madaki Kunci ne ya bayyana hakan ya yin da yake zantawa da KANO FOCUS ranar Alhamis.

Madaki ya ce basa kokwanto kan zargin da suke yi a kan mutanen uku, acewarsa ba za su bar abin ya tafi hakaba, ba tare da daukar mataki ba.

“Abdullahi Abbasa da Honorable Khalid Diso, da Gwarmai  S A sun jagoranci gungun wasu matasa yan bata gari zuwa wannan ofis inda suka faffasa kuma saka sa wuta a wannan waje”

Ya ce tuni suka fara hada bayanai kuma da zarar sun kammala za su shigar da kara a kotu.

Yadda al’amarin ya faru.

Da safiyar yau ne wasu matasa dauke da muggan makamai suka farwa ofishin jam’iyyar APC na jihar Kano tsagin Malam Ibrahim shekarau, wanda mallakin Sanata Baraune.

Matasan sun cinna wuta a wurare da dama na ofishin tare da farfasa gilasansa da kuma sace wasu muhimman abubuwa da ke cikinsa.

Muhammad Shehu shaidar gani da ido ne ya ce matasa sun fito ne daga harabar Sakatariyar Audu Bako, suka kuma bi kan titin Sokoto suka bullan kan titi Maiduguri.

da ga nan ne kuma suka isa inda ofishin ya ke suka kuma sa duka tare da cinna wutar.

“Matasa ne aka turosu da makamai da galan galan na fetur zuwa ofishin nan na Barau, kawai sun sa duka sun faffasa wajen sun saci kujeru.

“Abinda zai baka haushi wai motar ‘yan sanda na binsu a baya daya gaba daya a baya, akwai ma ‘yan sandan da na sansu da idona.

“Jami’an gwamnati muke zargi da turosu, su ne nan suka sakasu yin wannan aikin.

Shi ma Ibrahim Jamilu ya ce a gabansa matasan suka isa ofishin dauke da makamai masu tarin yawa, suka kuma sa duka kan mai uwa da wabi.

“Harga Allah a gabana suka zo sun kai su kunsan dubu da adduna da wukake suka fara kona wurin.

“Nan take muka fara waya muna kiran mutanenmu, muna gaya musu su zo za a kona ofishin Barau.

“Suna ganin mun fara yawa ne kuma sai suka fara guduwa daga wurin. Acewarsa.

Yadda na sha da kyar

Isma’il Muhammad da ke gadin ofishin ya ce ba dan ya buya a bandaki ba da tuni matasan sun kashe shi.

Ya ce Allah ne kadai ya kubutar da rayuwarsa, ya sa ya kewaya bayan ofishin, basu same shi a ciki ba.

“Na gansu dauke da makamai masu tayar da hankali da suka kidimanin rayuwa.

“Sun shigo da fetur ne a galan, ai idan aka ce maka adadinsu ya kai dubu bazan musaba, sai da na gudu fah, karshe a bandaki na buya.

“Ta kan titin Maiduguri suka bullo babban tititin da ko shaidan ne ya biyo sai an ganshi, sai daga baya kuma yan sanda suka zo.

Abdullahi Abbas yaki magantuwa

A kokarin jin ta bakin Abdullahi Abbas kan zargin da ake yi masa mun ziyarci gidansa, inda aka ce bai sakko ba.

Bayan mun jira ne kuma ya fita zuwa filin jirgin sama domin zuwa Abuja.

Mun kuma bishi har filin jirgin saman sai dai hakanmu bai cimma ruwa ba domin yaki cewa komai.

An kama mutum 13

Rundunar yan sandan jihar Kano ta ce ta kama mutane 13 cikin masu tada husumar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar da tsakar ranar Alhamis.

Ya ce an kamasu da nau’in makamai iri-iri, da suka hadar da wukake, da gorori, gariyo da barandami.

Kiyawa ya ce tuni kwamishinan ‘yan sandan Kano Shu’aibu Sama’ila Dikko ya bayar da umarnin a fadada bincke kan al’amarin.

Sakatariyar Audu Bako ce matattarar ‘yan daban

An dai ga matasan sun fito daga sakatariyar Audu Bako dauke da makaman, inda suka bi kan titin Sokoto, zuwa Cinimar  Marhaba suka bulla kan titin Maiduguri.

Haka zalika bayan kammala aikinsu an gansu sun koma cikin sakatariyar suna sauya kaya, daga nan suka tafi gida.

Haka zalika an ga yadda suka dinga fada da junansu bayan fitowa daga Sakatariyar harma aka jikkata wani matashi da aka yasar bakin hanya.

Matashin dai ya sha suka da wuka a wuyansa da kansa, inda jini ke kwarara, amma aka ransa wanda zai kai masa dauki.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

FG kickstarts construction of Emerging Technologies Institute in Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

As part of significant milestone in the Federal Government of Nigeria’s efforts to secure the socio-economic wellbeing of the future generation, as the ground was opened for commencement of construction of the Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI) under the aegis of the National Agency for Science and Engineering Infrastructure (NASENI), The Presidency.

 

KKANO FOCUS reports that the Executive Vice Chaiman/Chief Executive Officer (EVC/CEO) of NASENI, Mr. Khalil Suleiman Halilu during the Ground-breaking ceremony held at the Bayero University Kano (BUK) New Campus said the new institute sits on 30 hectares of the BUK land to be built, featuring state-of-the-art facilities, including innovation hubs devoted to Artificial Intelligence and other cutting-edge technologies, complemented by reliable power supply. “NASENI will fully build and equip and support the new Institute” said the EVC/CEO.

 

The future of socio-economic development for nations rests on human creativity, innovation and cooperation, Artificial intelligence, robotics amongst others.

 

Halilu said that the establishment of SETI in Nigeria is to rapidly respond to the waves of young people globally revolutionizing world economies with unprecedented emergence of socio-economic frontiers as by-products of innovations and ingenuities of these young minds.

 

“We in NASENI are firm believers in the potential of young Nigerians to be the prime catalysts of the type of transformation that Nigeria requires. And we will do everything within our powers to support them to fulfil this important responsibility”

 

“We are gathered here today to kickstart a project that will transform the lives and careers of future generations of young Nigerians. The Sustainable & Emerging Technologies Institute (SETI), located at the Bayero University Kano (BUK) by NASENI. This is very much in line with our operating principles; what we call our 3Cs: Collaboration, Creation, and Commercialization. These 3Cs are the principles that passionately drive us and guide the work that we do to ensure the industrialization of Nigeria in line with the Renewed Hope agenda of President Bola Ahmed Tinubu.”

 

SETI will produce innovators, technologists, entrepreneurs who will make their mark not just in Nigeria but around the world. “I’m eagerly looking forward to the day, not too long from now, when the Institute’s first set of beneficiaries will astonish the world with what they’re capable of accomplishing. These stories will put not just BUK on the global innovation map, but also Kano State and the entire Nigeria” said Halilu.

 

While carrying out the symbolic foundation laying ceremony of the institute as Special Guest of Honour, the Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, described the project as not only laudable but NASENI’s another way of fast-tracking  the placing of Nigeria on the global map of innovation and industrialization. The minister called the project an “ace project” and a pointer to secure a veritable socio-economic development for the nation.

 

In his goodwill message, the Vice Chancellor of BUK, Professor Sagir Adamu Abbas described the new institute as a vehicle for bringing together the three critical tripods for economic and sustainable development for nations, that is, the government, academia and industry. He described the ground-breaking event as the beginning of Nigeria’s journey in pursuit of sustainable development, massive job creation opportunities for the youths, and that the BUK was delighted to be host to such laudable initiative and momentum.

 

There is also, in addition to SETI, a second NASENI project for BUK is an Agri-preneurship Training Hub, that will be equipped with modern greenhouses, and facilities for Soil-less Farming, and Tissue Culture; occupying 10 hectares of land at the Old Campus. These projects collectively represent what NASENI stands for, that is, building capacity, advancing industrialization, supporting economic growth and prosperity.

 

NASENI appreciates the Government and people of Kano State, and the Vice Chancellor, management and students of Bayero University Kano (BUK), for all the support. Special gratitude goes to the Honourable Minister of Innovation, Science and Technology, Chief Uche Geoffrey Nnaji, the Special Guest of Honour.

 

NASENI thanked members of the National Assembly for their support, especially the NASENI oversight Committees in both chambers. And of course, President Bola Ahmed Tinubu, who has given NASENI the opportunity to serve Nigeria through his unwavering demonstration of commitment to the success of the Agency.

Continue Reading

Hausa

Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Published

on

Jaafar Jaafar

 

Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.

 

Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

 

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.

 

Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!

 

Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.

 

Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.

 

Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.

 

Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.

 

Allah Ya zaunar da mu lafiya.

Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook. 

 

Continue Reading

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Trending