KANUN LABARAI
Gwanda mu auri yayyen iyayenmu da mu auri samari marowata- Yan mata a Kano
Rafi’atu Ilyasu
Ƴanmata a Kano sunyi barazanar daina auren samari, sakamakon shiga ƙungiyar samari marowata, inda suka ce gwara su auri sa’anni iyayensu masu sakin aljihu.
Kano Focus ta ruwaito tun bayan da samari suka fara dunƙule hannu da rufe bakin aljihu ne, ‘yanmata suke ta cece-kuce a kan lamarin.
Har ta kai yanzu an fito d wasu kungiyoyi na marowata da ke koyar da tsuke bakin aljihu ga samari, da hana yan mata kudi duk da sunan yin hakan almubazzaranci ne.

A zantawar Kano Focus da wasu ‘yan mata a nan Kano sunce dasu auri mai dunkule hannu gwara su auri dattijo mai sakin hannu koda ya girmi ubansu.
Siddiqa Sadi Muhammad wata budurwace da ke zaune a unguwar Tudun yola, ta ce babu kira ba abinda zaici gawayi, ta ce matukar saurayinta ya shiga kungiyar za ta bashi dama ya fita.
Sai dai ta ce idan ya kekasa kasa ya ki ficewa to shakka babu za ta watsar dashi ta kuma nemi mai sakin aljihu.
“Wallahi babu ƙira babu abin da zai ci gawayi, muddin saurayina ya shiga wannan ƙungiya to zan bashi dama ya fita.
“Idan yaƙi fita zan iya rabuwa dashi, kuma idan na samu wanda hannunsa da aljihunsa ba a dunƙule ba, zan yi wuf da dashi ko da kuwa ba saurayibane.”
Ita kuwa Maimunatu Ɗahir Yunus da ke zaune a unguwar Sauna Kawaji, dake karamar hukumar Nasarawa,cewa tayi ko kadan bata amince da tsarin ba.
“Mu mata ba aikin yi ne damuba, samarin sune ke saka mana data, su ne suke saka mana kati don kiran a bokan arziƙi.
“Haka kuma su ne ke bamu kuɗin da mukeyin anko, su suke siya man kayan kwalliya, da abubuwan da ba za a rasa ba.”
“Idan a kace sun dunƙule hannunsu, tayaya zamu samu waɗannan abubuwa.
“Indai za su dunƙule hannu muma zamu ɗauki matakin da ya dace, kinga kenan sun daina zuwa hira gidanmu, kowa ya zauna a inda yake.”
“Har ga Allah in dai za a ɗora da wannan doka, to har dani a cikin ƴanmatan da za su sha wahala.”
Sheikh Ameer Sarki shi ne shugaban kungiyar samari marowata ta Kano, a zantawarsa da Kano Focus ya ce an kafa kungiyar ne domin kawar da almubazzaranci a cikin jama’a.
Ya ce manufar kafa kungiyar shi ne yaki da barnar kudi ba gaira ba sabar da samari ke yi akan ‘yan mata.
Ya ce jama’a basu fahinci manufar kungiyar ba ne, shi yasa suke yi mata wani kallo na daban.
“Maƙasudun wannan ƙungiya shi ne, kare mutuncin mata, domin wannan ƙungiyar babu wanda tayiwa gata sama da mata, sabo da gudun tozarci ko yaudara.”
“Mata a kan kansu suna cewa: ‘kiji tsoron namijin da zaizo yana kashe miki kuɗi’ a ƙarshe zakiga yana da wata manufa a kan ki.
Ameer ya cigaba da ce wa, kashe-kashe kudin ke rudar mata na fadawa matsala da ke rushe musu tarbiyya.
“Amma idan mutum ya dunƙulle hannunsa, ya rufe bakin aljihu, baima kashe miki kuɗi ba, bare yazo miki da wata maganar banza.
“Daga sanda muka aure mace, dole mu buɗe mata bakin aljihu, saboda muna shan zagi yanzu a gunsu, wasu ma sun daina kulamu.”

Hausa
Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Aminu Abdullahi
Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.
A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.
Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.
Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.
Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.
Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.
Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.
Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.
A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.
Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.
Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.
“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya. Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan. Ina mai matukar mika godiya da gareku.
“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.
A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.
Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Headlines
Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Aminu Abdullahi
Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice, Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.
According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police, Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4) respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.
“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million
“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda, raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.
“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.
“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.
“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.
“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Hausa
Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Jamilu Uba Adamu
An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.
Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;
“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”
Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki, daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.
