Connect with us

KANUN LABARAI

KANSIEC na neman cinye mana hakkokinmu-jami’an zaben kananan hukumomi

Published

on

Aminu Abdullahi

Makwani uku da gudanar da zabukan kananan hukumomi a jihar Kano amma har yanzu ba a biya wadanda suka gudanar da aikin zaben hakkinsu ba.

A zantawa ta musamman da jaridar Kano Focus wasu daga cikin wadanda suka gudanar da aikin sunce har yanzu hukumar bata waiwayesu ba kan batun biyansu hakkokin nasu.

Balaraba Musa na daga cikin wadada suka gudanar da aikin zaben yace hukumar ta ce za ta biya su hakkokinsu kwanaki biyu bayan kammla zaben ne, sai dai har yanzu shiru kake ji.

“Nayi aiki ne a mazabar Zaitawa dake Karamar Hukumar Birni, a kwati mai lamba 014.

“Ina kira ga gwamnati da ta taimaka ta biyamu hakkokin mu,” a cewar ta.

Itama Zainab Ibrahim ta ce duk da cewa ta fito a kan lokaci zuwa inda aka turata amma har yanzu shiru take ji malam yaci shirwa.

“Nayi aikina ne a mazabar Shahuci da ke Karamar Hukumar Birnin

“Sanda zamuyi aikin sunce za su tura mana da kudaden mu asusun banki,” a cewar ta.

Haka kuma Abdulsalam Abubakar da ya yi aikin zabe a mazabar Tukuntawa ya ce a ka’ida sati daya da yin zabe za a biyasu hakkokin su, amma har an shiga sati na uku ba tare da jin wani labariba.

“Wasunmu dalibaine, gashi yanzu an koma makaranta amma ba a biya mu ba,” inji shi.

Kudinmu za su iya salwanta 

Isah Abdullahi da ya yi aikin zabe a Mazugal dake karamar hukumar Dala ya ce yana tsaron kada hukumar zabe ta hanasu hakkokinsu baki daya.

Ya kara da cewa bai kamata a ce hukumar zaben tayi jinkirin biyan su hakkokinsu ba duba da cewa sun fita guraren da aka tura su akan lokaci kamar yadda aka umarce su.

Ya kuma ce sun bi dukkan matakan da suka da ce don ganin an biyasu hakkokinsu, sai dai har yanzu shiru suke ji.

“Indai muka je sai suce mukara hakuri zamu ji alart, gaskiya muna fargabar kada su cinye mana kudaden mu, ” a cewar sa.

Ba ma so a sake cinyewa wasu kudi ne

Sai dai hukumar zabe ta jihar Kano KANSIEC ta matsalar da aka samu ayin zaben da aka gudanar a baya ce ta sanya jinkirin.

Mai magana da yawun hukumar Dahiru Lawan Kofar Wambai ya ce a shekara 2018 an samu matsaloli na son zuciya daga gurin turawa zaben kananan hukumomi.

Ya ce a wancan lokacin turawan zabe aka baiwa kudaden ma’aikatan wucin gadi a hannu, don su biya su amma a karshe da yawan wadanda suka yi aikin ba a biya su hakkokinsu ba.

Ya kara da cewa hakan tasa a wannan karon hukumar zabe tayi tsari, ta yadda duk wanda ya yi aiki zai samu hakkinsa ba tare da an rage masa wani abu ba.

“A yanzu muna kan tantance lambobin asusun bankin wadanda suka yi aikin ne don gudun kada a samu matsala.

“kowa za a biya shi hakkinsane ta lambar asusun bankin da ya bayar nan bada jimawa ba,” a cewar sa.

Sai dai a duk bayanin da yayi bai bayyana lokacin da za su biya ma’aikatan ba.

Idan za a iya tunawa dai ko a shekarar 2018 akwai ma’aikatan wucin gadin da suka gaza samun hakkokinsu na ayyukan zabe da suka yi.

Wadanda kuma har yau dinnan ba su samu ba, hakan ta sanyan galibinsu ke tsoron kar a cinyemsu.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Shugabannin Fulani sun goyi bayan takarar Tinubu

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

Shugabannin Fulani wato (Ardo) daga sassa daban-daban na Najeriya sun jaddada goyon bayansu ga dan takarar jam’iyyar APC Sanata Bola Ahmed Tinubu a wani taro da suka gudanar a babban birnin tarayya Abuja a ranar lahadi.

A taron da suka yi tare da hadin gwiwar Kungiyar Sabuwar Arewa wato “Arewa New Agenda” shugabannin sun yi alkawarin yin amfani da ‘yan kungiyar 33,661 wajen tattaro sauran ‘yan uwansu Fulani domin su zabi Sanata Bola Tinubu.

A lokacin da yake nasa jawabin bayan an kammala al’adar Fulani ta rabon goro ga mahalarta taron, shugaban Kungiyar Aliyu Liman Bobboi ya ce raba goron da aka yi yana nufin shugabannin za su koma gida su isar da sakon shawarar da aka yanke a wajen taron zuwa ga mabiyansu.

Ya kara da cewa taron an gudanar da shi ne domin su nuna wa duniya goyon bayansu ga Tinubu saboda sun yarda, sun kuma yi amanna da cancantarsa, suna kuma masu adduar samun nasara a zabe mai zuwa.

Ya kara da cewa Ardo a matsayinsu na shugabanni suna da ta cewa sosai akan wanda mutanensu zasu zaba, kuma suna da yakinin cewa magoya bayan nasu za su yi ma su biyayya.

Liman ya yi nuni da makusanta shakikai dake tareda Tinubu kamar Gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje, Abubakar Badaru na jigawa, tsohon shugaban EFCC Malam Nuhu Ribadu, da sauran manyan Fulani yace wannan na nuni ga yadda Tinubu ya dauki kabilar ta Fulani da muhimmanci.

Kungiyar ta shuwagabannin Fulani ta kuma bawa Tinubu sarautar Barkindo.

Gwamnan jahar kano Abdullahi Umar Ganduje da yake bayani ya yi tsokaci akan irin bajinta da kwarewa da kuma cancantar Tinubu da ya shugabanci Najeriya. Ya kuma kara da cewa Fulani a matsayinsu na kabila dake fuskantar barazana a sassa daban-daban, suna bukatar zabar shugaban da zai iya basu kariya.

Ganduje ya kara da cewa suna nan kan kokarin samarwa Fulani da wani tsari wanda zai bunkasa hanyoyin kiwo a duk fadin kasar nan.

A nasa bayani dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Sanata Tinubu ya yi tsokaci akan irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsa da mahaifiyarsa a bangare daya da kuma Fulani a dayan bangaren. Ya nuna cewa alakarsa da Fulani amana ce ta dindindin.

Ya kara jaddada niyyarsa ta samarwa Fulani hanyoyin kiwo na zamani da za su kawo cigaba da kuma yalwa ba tare da tsangwama ba.

Tinubu ya kara da cewa bai taba tsammanin zai hadu da bafulatanin da ya fi shi jin yaren yarbanci ba sai gashi yau ba zato ba tsammani ya hadu dasu. Ya ce wannan abun a yaba ne.

“Wannan itace irin Najeriyarda muke bukata, kasa daya al,umma daya.  Ina mai tabbatar maku idan da zamu kasance anan tsawon sa,o,I biyar iyakacindai zancenda zakucigaba da ji daga gareni kenan.  Ina mai matukar mika godiya da gareku.

“Tabbas makiyayan Najeriya na fama da matsaloli dabban dabban amma ina mai tabbatar maku da cewa munada tsari na musamman da zai magance wudannan matsalolin,’ a cewar Tinubu.

A nasa jawabin Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Tinubu a matsayin mutumin da ya cancanta, ya dace wanda kuma zai iya kawo ci gaba mai dorewa ga kabilar ta Fulani.

Ya kuma yi godiya ga goyon bayan da suka bashi tareda alkawarin ba zai ba su kunya ba.

Continue Reading

Headlines

Police In Kano arrest two kidnappers, rescue victims

Published

on

Aminu Abdullahi

 

 

 

Kano state police command has arrested 22 year old Nura Auwal, of Rijiyar Lemo Quarters, and his accomplice,  Abubakar Lawal, of Bachirawa Quarters, for the kidnapping of 3 year old Umar Isyaku (3) and 4 year old Aliyu Auwal.

KANO FOCUS reports that the two kidnappers of the children demanded for N20 million ransom, but later settled for N2 million with their parents.

According to Kano state police Command spokesman, Superintendent of Police,  Abdullahi Haruna Kiyawa: “On 26 January, 2023, reports were received from one Isyaku Salisu and Auwal Sale residents of Bachirawa Quarters, Ungogo LGA, Kano State that their children, Umar Isyaku, (3)and Aliyu Auwal (4)  respectively were kidnapped, and handwritten letters with mobile phone numbers and bank account details were sent to them for communication and payment of ransom.

“N20 million was demanded but later settled at Two Million Naira N2 million

“On receipt of the reports, the Commissioner of Police, Kano State Command, CP Mamman Dauda,  raised and instructed teams of Operation Restore Peace led by SP Aliyu Muhammad Auwal, Officer in Charge of Anti-Kidnapping Squad, State Criminal Investigation Department, Kano State Command to rescue the victims and arrest the culprits.

“The teams simultaneously swung into action. Sustained efforts coupled with intelligence-led operations resulted in the arrest of two suspects: one Nura Auwal, (22) of Rijiyar Lemo Quarters Kano, and his accomplice, one Abubakar Lawal, (22) of Bachirawa Quarters Kano.

“Victims were rescued unhurt at an uncompleted building.

“On preliminary investigation, the suspects confessed to having conspired and kidnapped the two children and sent letters to their parents with phone numbers and bank account details requesting a ransom.

“Suspects will be charged to court upon completion of the investigation.”

Continue Reading

Hausa

Samba Kurna da Good Boys Dorayi za su fafata a wasan karshe na ‘Ahlan cup’

Published

on

Jamilu Uba Adamu

An kammala Shirye-Shiryen gudanar da wasan karshe na gasar cin kofin  Kwallon kafa na “Ahlan Cup’ tsakanin Samba Kurna da Good Boys Dorayi.

Wanda yake jagorantar gasar Alh. Abubakar Tsoho Musa Rijiyar Zaki ne ya bayyana wa manema labarai cewar;

“Kungiyoyin Kwallon Kafa talatin da biyu ne (32) suka fafata a gasar, wacce aka gudanar a wasannin sili daya kwale (knock-out ). An Kuma buga wasa talatin ne. Inda Kungiyar Kwallon Kafa ta Samba Kurna da Good Boys Dorayi sukai nasarar zuwa wasan karshe.”

Za dai a fafata wannan wasa a ranar lahadi 7 ga watan Augusta da misalin karfe hudu na Yamma a filin Wasa na Makarantar sakandiren Unguwar Rijiyar Zaki

Kuma ana sa ran wasan zai samu hallatar manya- manyan baki,  daga ciki da wajan jihar Kano a karkashin jagorancin Shugaban Hukumar wasan Kwallon Kafa ta Jahar Kano Dr. Sharu Rabiu Inuwa Ahlan.

Continue Reading

Upcoming Events

There are no upcoming events at this time.

Facebook

Twitter

Trending