Connect with us

Hausa

Yadda aikin titin Dandishe ke shirin hallaka al’ummar yankin

Published

on

Aminu Abdullahi

Al’ummar Unguwar Dandishe da ke karamar hukumar Dala a nan Kano sunce suna kamuwa da cutuka iri-iri da suka hadar da Athma, sakamakon kwazazzabon da aka haka musu da sunan gyaran titi.

Haka zalika sun ce matansu na yin bari, ko kuma su haihu nan take da zarar an dauke su zuwa asibiti saboda rashin kyawun hanyar.

A wani bincike da jaridar Kano Focus ta gudanar ta gano yadda aikin ginin titin da ya tashi daga Dandishe, zuwa  Gobirawa yabi ta Tudun Fulani ya bulle a Bachirawa ya zame musu jangwam.

A cewar al’ummar yankin ginin titin na haifarmusu da cutuka da dama wadanda a da basu da su da suka hadar da Asthma, mura mai zafi da wasu cutuka da har yazu ba su kai ga gano su ba.

Haka zalika sun ce da wuya a dauko mace mai juna biyu da ga farkon titin zuwa karshensa, bata zubar da cikinba ko kuma ta haihu a kan hayar.

Annur Ahmad Muhammad wani mai yin sana’a ne a gefen titin, ya ce an dawo da aikin titin ba da jimawaba, kwatsam sai aka nemi masu aikin aka rasa.

Ya ce matafiya da wadanda ke sana’a a gurin nashan wahala, da hakan yasa masu cutar asma ke tashi a duk lokacin da suke tafiya a titin.

Umar Ashir Alhassan cewa ya yi basu ji dadin yadda gwamnati ta tsaida aikin ba.

Ya ce wasu lokutan mata kanyi bari, ya yin da ake kaisu asibiti sakamakon lalacewar da hanyar tayi.

Ya kara da cewa gyara titin zai saukaka yawan cunkoso da ake samu a babban titin kurna.

Da gangan gwamnati ta tsayar da aikin

Haka zalika al’ummar yankin sun zargi gwamnatin Kano da tsayar da aikin da gangan.

Acewarsu dan kwangilar dake aikin titin ya kwashe motoci da kayayyakin aikin a makonnin da suka gabata.

Titin na Dandishe mai tsahon kilomita shida ya shafe shekaru biyar a lalace har yanzu kuma an kasa kammala shi

Idan za a iya tunawa dai a karshen shekarar 2020 ne akadawo da aikin gyaran titin kafin daga bisani a farkon shekarar 2021 dan kwangilar ya kwashe kayan sa.

Ko da yake wasu majiyoyi sun ce rashin biyan dankwangilar hakkokin sa da gwamnatin tayi ne yasa ya dakatar da aikin.

Ba mu san dan kwangilar ya gudu ba

Ko da Kano Focus ta tuntubi kwamishinan ayyuka na jihar Kano  Idris Garba Unguwar Rimi ya ce basu da masaniyar dakatar da aikin.

Unguwar Rimi ya ce basu san dan kwangilar ya dakatar da aikin titin ba.

A cewarsa sunyi yarjejeniya kan cewa za a kammala aikin kafin lokacin damina.

Ya kara da cewa zai gayyaci dankwangilar domin jin dalilin dakatar da aikin ginin titin.

Ya kuma baiwa al’ummar yankin hakura, acewarsa za su tabbatar an kammala aikin kafin zuwan lokacin damina.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Published

on

Jaafar Jaafar

 

Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.

 

Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

 

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.

 

Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!

 

Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.

 

Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.

 

Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.

 

Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.

 

Allah Ya zaunar da mu lafiya.

Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook. 

 

Continue Reading

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Hausa

Gov. Yusuf Directs Reassigned Commissioners to Handover and Assume Duties by Tuesday, 17th December

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

The Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, has directed all reassigned commissioners to ensure a smooth handover and assumption of duties by Tuesday, 17th December 2024.

Speaking through his spokesperson, Mr. Sanusi Bature Dawakin Tofa, the Governor stated that the cabinet changes will take full effect during the next council meeting on Wednesday, 18th December 2024.

He emphasized the need for the completion of all transition processes before then.

“All commissioners affected by the changes are directed to hand over their responsibilities between Monday, 16th and Tuesday, 17th December 2024,” the statement reads.

The Governor further urged members of the state executive council to redouble their efforts and uphold a strong spirit of teamwork, dedication, and commitment to supporting his administration in serving the good people of Kano State.

Continue Reading

Trending