Connect with us

Hausa

An bude kamfanin leken asirin masoya da ma’aurata a Kano

Published

on

Aminu Abdullahi

Wani matashi, Sulaiman Muhammad ya bude kamfanin leken asirin masoya da ma’aurata a Kano.

Kano Focus ta ruwaito matashin wanda dalibi ne a jami’ar Bayero da ke nan Kano ya kirkiro sana’ar ne domin yiwa ‘yan mata ko matan auren leken asirin abinda mazajesu ko matayensu ke aikatawa a lokacin da basa tare.

Ya ce mace za ta iya basu kwangilar bibiyar inda mijinta ko saurayinta ke zuwa, don sanin ko yana yi mata karya.

Haka zalika ya ce idan har miji ya cewa matar sa ya tafi gurin aiki to su kuma za su bibiya su gano gurin aikin ya tafi ko wani gurin na daban.

A cewarsa duk wanda ya ke so a yi masa irin wannan leken asiri to zai biya kudi a mataki uku.

Matakin farko za a biya N10,000 domin sa ido jigari-jigari, sai kuma mataki na biyu da za a biya N15, 000 domin tsanantawa ba kamar na baya ba.

Haka zalika mataki na uku wanda shi ne babban za a biya N25,000 domin binciken kwakwkwafi da kuma bin diddigin halin wanda ake bukata ke ciki.

Sana’a ko munafurci

To sai dai bullar wannan sabuwar sana’a ce  samari da ‘yan mata a Kano suka  bayyana ra’ayoyinsu, inda wasunsu ke kallonta a matsayin munafurci zalla.

Aisha Taiyo Ibrahim mai shekaru 23 da ke zaune a unguwar Hotoro ta ce sana’ar leken asiri ta saba ka’ida.

A cewarta idan duk abinda mutum ya yi za a dinga bibiyar sa to hakan zai haddasa zargi da rashin fahimta a tsakanin masoya.

Bakin talauci yasa an bude tashar ‘Buhari’ a Kano

Gwamnatin tarayya ta amince a bude sabbin jami’o’i uku a Kano

Kungiyar ‘yan gwanjo ta gudanar da adduo’in neman zaman lafiya a Kano

Ta kara da cewa bai kamata a ce mace ta sa ana bibiyar inda saurayin ta ko mijinta yake zuwa ba.

” Yanzu ka sanar da ita zaka je gurin aiki sai a gurin aikin akace ka biya ta wani gurin.

“To su inda suka ga ka tsaya nan za su fada mata tunda ba za su san dalilin da ya tsaida kai ba.

“Daga nan kuma zargi zai shiga sai alaka ta lalace gaskiya ni bana goyan baya, domin a addinance da kundin tsarin mulki duk sun haramta haka,” a cewar ta.

Rukayya Adam mai shekaru 24 daliba a jami’ar Yusuf Maitama Sule ta ce bata goyan bayan yin leken asiri ga miji ko saurayi.

“Kazantar da baka gani ba ai tsafta ce, shi namiji yana da hanyoyi kala-kala,, gwanda dai kowa yaji tsoron Allah kawai.

“Kuma su masu irin wannan sana’ar za su iya bada abinda ba gaskiya bane akan mutum, kaga daga nan sai zargi ya shiga ciki,” a cewar ta.

Habiba Abu Haruna mai shekaru 24 da ke unguwar Jambulo cewa tayi rashin basira ne mace tasa ana bibiyar mijinta domin wataran za ta tono abinda bata sani ba.

Ta kara da cewa gwara a cigaba da tafiya a haka don gudun kada a tono abinda ba zai yiwa kowa dadi ba.

“Koda zai yi  karya, kansa yayiwa, yanzu kaduba yadda mata ke kashe mazajen su ta hanyar yin bincike a waya, ina kuma a ce sawa suke ana bibiyar sa kaga abin sai yafi haka,” inji ta.

Mika’il Yunus wani magidanci da ke unguwar Hausawa mai shekaru a shirin da bakwai ya ce ko kadan ba zai iya sawa a dinga bibiyar abokiyar zaman sa ba.

“Wannan ai ba sana’a bace munafurcine don ko turawa basa yin haka balle mu hausawa kuma musulmai.

“Ni ina ganin kamata ya yi su canza sana’a amma ba wannan ba, don wannan ba abinda za ta kara sai rigingimu a tsakanin masoya,” a cewar sa.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

Illar siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya a jihar Kano

Published

on

Jaafar Jaafar

 

Na jima ban ga tsantsar rashin kishi da cin amanar aiki da ya wuce ƙaryar da hukumar yansandan jihar Kano ta gilla ba saboda tsananin siyasantar da harkar tsaro da zaman lafiya da cigaban al’umma.

 

Babu wani rahoto na sirri kan wani mugun abu da ke faruwa a birni ko ƙauye wanda gwamna bai san shi ba. A wasu lokutan ma gwamnan ya kan riga jami’an tsaro samun wani rahoton sirrin. Duk wanda ya san yadda “special service directorate” (wadda ke karkashin ofishin gwamna) ke gudanar aiki, zai fahimci inda na dosa.

 

Kasashen da su ka ci gaba, ba sa wasa da duk bayanin da hukumar yansanda ta fitar. Domin su a kasashen su dansanda shi ya fi kowa adalci, shi ya sa zai wahala yansanda su tuhume ka da laifi ka ga alkali bai ɗaure ka ba.

 

Kafin harin Boko Haram na farko a Kano a ranar 20 ga Janairu 2012, akwai wani babban jami’in gwamnati da ya faɗa min cewa ƙasar Amurka na duba yiwuwar buɗe ƙaramin ofishin jakadanci (consulate) a Kano wanda zai riƙa ba da visa da gudanar da wasu shirye-shirye a jihar Kano. Kwatsam sai a ka kawo harin bam. Daga nan maganar ta mutu murus. A tunaninka in da a ce Amurka za ta sake duba yiwuwar bude consulate a Kano, sai ta ji sanarwar hukumar yansanda ta fitar, me ka ke tunanin za ta yi? Za ta fasa ne!

 

Haka fa muna ji muna gani British Council ta rufe cibiyarta da ke Kano. Wannan cibiya ta taimaka gaya wajen sa wa matasa sha’awar karatu, kuma ta samar da damarmaki na karatu da tafiye-tafiyen nazari kasashe ga mutane da dama. Ita ma wannan cibiya a dalilin rashin tsaro yanzu ta tattara inata-inata ta tafi.

 

Ta fuskar kasuwanci, watakil wannan sanarwar karyar da hukumar yansanda ta fitar ta sa masu son zuba jari daga wasu wurare (foreign investors) su fasa. Haka zalika, watakil wannan asarar ta sa masu zuwa fatauci kasuwannin Kano su ja jiki. Ka ga sun jawo wa yan kasuwa da jihar asara.

 

Tarihi ya nuna tun kafin Kano ta yi shuhura a harkar kasuwanci, Katsina ita ce cibiyar kasuwanci a kasar Hausa. Babban abin da ya sa Katsina ta koma baya shi ne yaƙe-yaƙe da ta sha fama da shi, musanman a ƙarni na 18.

 

Kira na ga gwamnatin jihar Kano shi ne kada ta bar wannan cin amana ya wuce ba ta yi wa tufkar hanci ba. Kamata ya yi gwamna da kan shi ya kira gagarumin taron zantawa da yanjarida wanda ya ƙunshi manyan gidajen jaridu na ƙasa da waje domin fayyace wa duniya zancen. Idan ma da yiwuwar kai yandansan kotu, to yakamata gwamnati kada ta yi ƙasa a gwiwa.

 

Allah Ya zaunar da mu lafiya.

Jaafar Jaafar, shi ne mawallafim jaridar Daily Nigerian, ya kuma wallafa wannan rubutun ne a shafinsa na Facebook. 

 

Continue Reading

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Hausa

Gov. Yusuf Directs Reassigned Commissioners to Handover and Assume Duties by Tuesday, 17th December

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

The Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, has directed all reassigned commissioners to ensure a smooth handover and assumption of duties by Tuesday, 17th December 2024.

Speaking through his spokesperson, Mr. Sanusi Bature Dawakin Tofa, the Governor stated that the cabinet changes will take full effect during the next council meeting on Wednesday, 18th December 2024.

He emphasized the need for the completion of all transition processes before then.

“All commissioners affected by the changes are directed to hand over their responsibilities between Monday, 16th and Tuesday, 17th December 2024,” the statement reads.

The Governor further urged members of the state executive council to redouble their efforts and uphold a strong spirit of teamwork, dedication, and commitment to supporting his administration in serving the good people of Kano State.

Continue Reading

Trending