Connect with us

Hausa

Hadarin da ke tattare da wankan kududdufi lokacin azumi

Published

on

Aminu Abdullahi

A ya yin da zafin rana ke ci gaba da gigita matasa da ke yin azumi a Kano, da dama daga cikinsu sun zabi zuwa wankan kududdufi domin rage wahalar azumin.

A zagayen da Kano Focus ta yi wasu daga cikin kududdufai a nan Kano ta iske matasa da dama da ke yin iyo a cin ruwan domin ragewa kai zafin azumi.

Galibin matasan na zuwa kududdufan ne da zarar rana ta take ba kuma za su bar wurin ba sai yamma ta yi.

Kabiru Isah mai shekaru 35 dake wanka a ruwan garin Kumbotso ya ce yana zuwa ruwan kullum da zarar rana ta take.

“Ina zuwa wanka tun daga karfe biyu na rana zuwa karfe biyar na yamma sannan na koma gida.

“Idan na gama wanka akwai bishiyu a gurin da nake shimfida darduma ko tabarma na kwanta,” a cewar sa.

Shima Salihu Umar dan shekara 25 ya ce yana zuwa yin wanka kullum da yamma a ruwan hauren wanki.

“Wankan yana rage mana lokaci da kuma azabar zafin da nake ji a jiki na.

“Idan kana wanka za kaji wahalar azumin ta ragu sosai, kuma ba za kaji rana kamar yadda wasu ke ji ba

Muftahu Garba dan shekaru 18 da ke wanka a ruwan promise ya ce tun yana karamin yaro yake zuwa wanka kududdufin.

“Da na dawo daga makaranta muke tafiya ni da abokaina, kuma babu wanda ya taba jin wani ciwo,” a cewar sa.

Hadarin rama azumi 60

Sai dai malamai sun ce dukkanin wanda ke shiga ruwa domin yin wanka tsautsayi yasa ya sha ruwa to zai rama azumi sittin ne.

A cewar babban limamin masallacin juma’a na Usman bn Affan da ke Kofar Gadon Kaya, sheikh Abdullah Usman ba laifi bane mutum yayi wanka a ruwan idan har azumi yana bashi wahala.

Sai dai ya ce ya zaman wajibi a dinga kiyayewa ya yin da ake wankan don gudun kada azumin su ya karye.

“Idan har mutum yaji azumi na bashi wahala babu laifi ya yi wanka ko a ruwa, ko a bandaki.

“Babu wani nassi da yace haramunne yin wanka a ruwa ga mai azumi.

“Sai dai matukar ya bari ruwa ya shiga cikinsa dagangan to ba makawa sai ya rama azumi sittin.” inji shi.

Ya kara da cewa idan har ya zaman dole yin wankan to yana da kyau al’umma su dinga kiyayayewa don gudun abinda zai karya musu azumi da zai sanyasu kaffara.

Wanne mataki iyaye ke dauka

Wasu daga cikin iyaye da Kano Focus ta zanta dasu sun ce suna daukar matakai domin hana yaransu zuwa wankan kududufin.

Lawal Musa ya ce kwamitin tsaro na unguwar Gwale sun taba kama dansa yana wanka a ruwan kududdufi.

Sai dai ya ce tun daga lokacin yake daukar mataki don ganin dan nasa baije yin wanka ruwan ba.

Muhammadu Sani ya ce wani lokacin sakacin iyaye ne ke sawa ‘ya’yansu ke zuwa wankan kududdufi, da hakan ke sawa wani lokacin ya kai ga rasa rai.

Ya ce idan har iyaye za su dinga sanya ido akan ‘ya’yansu tare da bibiyar abokan da suke hulda da su to za a samu saukin al’amarin.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Hausa

EFCC arraigns one for N108 million fertiliser fraud in Kano

Published

on

Sanusi Hashim

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

The Kano Zonal Directorate of the Economic and Financial Crimes Commission, EFCC, has arraigned one Sanusi Hashim for allegedly misappropriating and converting to his personal use, the sum of 108 million Naira. 

 

KANO FOCUS reports that Hashim was arraigned before Justice Kabiru Dabo of the Kaduna State High Court sitting in Zaria on a one -count charge of misappropriation contrary to Section 293 and punishable under section 294 of the Penal Code.

 

He was alleged to have collected a total sum of 108 million Naira from one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer but instead misappropriated and diverted the money for his personal use.

 

The lone-count charge reads ‘’That you Sanusi Hashim sometime in April 2020 under the jurisdiction of the Kaduna State High Court dishonestly misappropriated and converted to your own use, the sum One Hundred and Eight Million Naira (N108,000,000) property of one Ahmad Mohammad Liman and Basiru Mohammad for the supply of fertilizer from Indorama Eleme Fertilizer and Chemicals and you thereby committed an offence under Section 293 and punishable under Section 294 of the Penal Code’’.

 

The defendant pleaded not guilty when the charge was read to him.

 

Counsel to the prosecution, Bright C. Ogbonna prayed the court for a trial date in view of the defendant’s plea.

 

Consequently, Justice Dabo remanded the defendant in a Correctional Centre and adjourned the matter to February 10, 2025 for hearing of bail application.

Continue Reading

Hausa

Gov. Yusuf Directs Reassigned Commissioners to Handover and Assume Duties by Tuesday, 17th December

Published

on

Mukhtar Yahya Usman

The Governor of Kano State, Alhaji Abba Kabir Yusuf, has directed all reassigned commissioners to ensure a smooth handover and assumption of duties by Tuesday, 17th December 2024.

Speaking through his spokesperson, Mr. Sanusi Bature Dawakin Tofa, the Governor stated that the cabinet changes will take full effect during the next council meeting on Wednesday, 18th December 2024.

He emphasized the need for the completion of all transition processes before then.

“All commissioners affected by the changes are directed to hand over their responsibilities between Monday, 16th and Tuesday, 17th December 2024,” the statement reads.

The Governor further urged members of the state executive council to redouble their efforts and uphold a strong spirit of teamwork, dedication, and commitment to supporting his administration in serving the good people of Kano State.

Continue Reading

Hausa

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta koma Northwest University, Kano

Published

on

Nasiru Yusuf Ibrahim

 

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar maidawa Jami’ar Northwest sunanta na asali, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

KANO FOCUS ta samo wannan sanarwa ne daga Keamishinan Ma’aikatar ilimi mai zurfi Dr Yusuf Ibrahim Ko far mata, a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook.

 

Dr Kofar Mata ya ce “A zaman majalisar zartarwar ta gwamnatin Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf na 21 yau Juma’a 29th November 2024 (27th Jumada Awwal 1446) ta amince da maidawa ta Jami’ar Northwest sunanta na baya, dogaro da dalilin da yasa aka kafata a shekara 2012.

 

“Sannan kuma don girmamawa ga Marigayi Dattijo uban ƙasa Dr. Yusuf Maitama Sule, an sawa sabuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari da cigaba da karatu sunansa.

 

“Sabuwar makarantar Yusuf Maitama Sule College of Education and Advanced Studies, Ghari, wacce aka amince da dokar gudanarwarta a zaman yau, babbar makarantace daidai da kolejin ilimi ta Rabiu Musa Kwankwaso dake Tudun Wada.

 

“Haka zalika makarantar Audu Bako Dambatta da kuma makarantar malam Aminu Kano mai laƙabin Legal. Dukkaninsu manyan makarantune don girmamawa da tunawa da manyan mutanen jihar Kano.

 

“Tuni majalisar zartarwar ta bada umarnin tura waɗannan dokoi zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano, harda gyaran shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu. Allah Ya taimakemu.”

 

 

Continue Reading

Trending